Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Douye Diri na PDP ya lashe zaɓen gwamnan jihar Bayelsa

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Mukhtari Adamu Bawa and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Turkiyya na shirin kafa asibitocin wucin-gadi a Masar don kula da Falasɗinawa

    Wani jirgin ruwan Turkiyya ɗauke da kayayyakin kafa asibitocin wucin-gadi, ya isa gaɓar ruwan Masar da ke kusa da mashigar Rafah.

    Jirgin ya taho da injinan lantarki, da motocin daukar marasa lafiya, da sauran kayan kula da lafiya zuwa gaɓar ruwan Al Arish da zimmar kafa asibitoci na wucin-gadi takwas, a cewar kamfanin labarai na AFP.

    Shi ne jirgin ruwa irinsa na farko da ya isa Masar, tun bayan fara yaƙi a Gaza ranar 7 ga watan Oktoba - lokacin da Hamas ta kai hari cikin Isra'ila tare da kashe aƙalla mutum 1,200 da kuma yin garkuwa da sama da 200.

    Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce asibitiin Gaza mafi girma na Al-Shifa "ya daina aiki". Sauran cibiyoyin lafiya na ba da irin wannan rahoton sakamakon ƙarancin lantarki, da man fetur, da kuma fargabar hare-hare.

    Wani jami'in lafiya na Turkiyya ya faɗa wa AFP cewa Masar ta bai wa ƙasarsu damar kafa asibitocin a yankin Al Arish, wanda ke da nisan kilomita 40 daga mashigar Rafah - wadda ta haɗe Masar da Zirin Gaza.

  2. Labarai da dumi-dumi, Douye Diri na PDP ya lashe zaɓen gwamnan jihar Bayelsa

    Gwamnan Bayelsa kuma ɗan takarar jam'iyyar PDP, Douye Diri, ya lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar da ta gabata.

    Mista Diri ya samu wa'adi na biyu ne bayan Baturen Zaɓe Farfesa Faruq Kuta ya bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara da ƙuri'a 175,196.

    Ɗan takarar adawa na APC, Timipre Sylva, shi ne ya zo na biyu da ƙuri'a 110,108, sai kuma Udengs Eradiri na jam'iyyar LP a mataki na uku da ƙuri'u 905.

    Sakamakon ƙaramar hukuma biyu na Kudancin Ijaw da Brass ne suka jawo ɗage tattara sakamakon har zuwa Litinin bayan an bayyana na ƙananan hukumomi shida cikin takwas a ranar Lahadi.

    Turawan zaɓe na wasu ƙananan hukumomi sun bayar da rahoton soke zaɓe a rumfunan zaɓe da dama saboda hatsaniya, da garkuwa da mutane, da sace malaman zaɓe.

    Kazalika, da yawa daga cikin wakilan jam'iyyun da ke cibiyar tattara sakamakon sun yi watsi da sakamakon da aka gabatar tun ranar Lahadi, amma babban baturen zaɓe na jihar ya nemi su kai ƙorafinsu ga Inec a hukumance.

    Zaɓen na Bayelsa ya fuskanci hatsaniya tun kafin fara kaɗa ƙuri'a, inda aka yi garkuwa da wata jami'ar hukumar zaɓe ta Inec kafin daga baya a sako ta.

    Inec ta sake fitar da sanarwar cewa an yi garkuwa da wasu jami'an nata a ƙaramar hukumar Brass, waɗanda ba ta bayyana adadinsu ba.

    Ƙuri'un da aka kaɗa

    Masu katin zaɓe: 1,560,862

    Masu zaɓen da aka tantance: 372,000

    Jimillar ƙuri'un da aka kaɗa: 291,212

    Ƙuri'un da aka soke: 3,658

  3. Yadda sakamakon zaɓen gwamnan Bayelsa yake zuwa yanzu

    Bayan kammala tattara sakamakon dukkan ƙananan hukumomi takwas na jihar Bayelsa, Gwamna Douye Diri na jam'iyyar PDP ne kan gaba a yawan ƙuri'un da aka kaɗa.

    APC da ɗan takararta Timipre Sylva ne ke biye masa, sai kuma Udengs Eradiri na LP a mataki na uku.

    Nan gaba kaɗan ake sa rana babban baturen zaɓe Farfesa Faruq Kuta zai bayyana wanda ya yi nasara a zaɓen na ranar Asabar.

  4. Zaɓen Bayelsa: Sakamakon ƙaramar hukuma ta ƙarshe ya iso

    Sakamakon ƙaramar hukumar Kudancin Ijaw ya isa matattarar sakamako ta zaɓen gwamnan Bayelsa da aka gudanar ranar Asabar.

    Jam'iyyar PDP mai mulkin jihar ce ta cinye ƙaramar hukumar.

    Masu katin zaɓe: 184401

    Masu zaɓen da aka tantance: 50153

    APC: 18174

    LP: 119

    PDP: 24685

    Jimillar ƙuri'un da aka kaɗa: 438321

    Halastattun ƙuri'u: 43158

    Ƙuri'un da aka soke: 663

  5. An ƙara kashe sojojin Isra'ila biyu a Gaza

    Isra'ila ta fitar da sunayen ƙarin sojoji biyu da aka kashe a faɗan da take gwabzawa da mayaƙan Hamas a Gaza.

    Sojojin da aka kashen su ne Isahar Natathan mai shekara 28 da kuma Itay Shoam mai shekara 21.

    Hakan na nufin Isra'ila ta rasa sojojinta 44 a yaƙin na Gaza.

    Isra'ilar ta kuma bayyana cewa ɗaya daga cikin sojojin nata ya samu mummunan rauni a faɗan da aka gwabza ranar Lahadi.

  6. Cikin sojojin Isra'ila da aka kashe har da ɗan fim ɗin Netflix

    Ana ci gaba da gudanar da jana'izar sojojin Isra'ila da aka kashe a hare-haren da take kaiwa ta ƙasa a Zirin Gaza a yau Litinin.

    An binne Sajan Sergey Shmerkin mai shekara 32 a Kiryat Shmona, wanda sojan ko-ta-kwana ne.

    Haka nan, an yi jana'izar Sajan Matan Meir mai shekara 38 a Odem, wanda yake cikin 'yan wasan da ke ɗaukar fim ɗin Netflix mai suna Fauda.

    Isra'ila ta ce zuwa yanzu an kashe sojojinta 44 a fafatawar da suke yi da mayaƙan Hamas ta ƙasa a Zirin Gaza.

  7. 'An harba makamai masu linzami zuwa cikin Isra'ila daga Lebanon'

    Hukumar tsaro ta Isra'ila ta ce an harba makamai masu linzami zuwa cikin ƙasar daga Lebanon.

    Ta ce an harbo makaman ne daga yankin Galilee, amma sun faɗa ne a wani yanki da babu kowa, kuma babu wanda ya jikkata.

    A wani saƙo ta shafin X, IDF ta ce dakarunta sun kai hari kan "wuraren tsare mutane na ƴan ta'adda" a Lebanon.

    Ana yawan samun artabu tsakanin dakarun Isra'ila da mayaƙa a kan iyakar Isra'ila da Lebanon a kusan kowace rana.

    Ana zargin mayaƙan Hezbollah da ke samun goyon bayan Iran da hannu.

  8. Gaza da safiyar Litinin a hotuna

    Fada ya ci gaba da gudana cikin dare a arewacin Gaza, yayin da mamayen Isra'ila na kasa ya ci gaba.

    Kungiyoyin ba da agaji sun ce fadan da ake ci gaba da yi ya sa duk wani kokari na amfani da hanyoyin ficewa daga yankin, ya zama abu mai hatsari.

  9. MDD na alhinin ma'aikatanta 101 da aka kashe a Gaza

    Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) na alhinin ma'aikatanta 101 da aka kashe a Zirin Gaza sakamakon hare-haren Isra'ila da ta ce tana kai wa mayaƙan Hamas tun ranar 7 ga watan Oktoba.

    "Kowanne daga cikinsu uwa ce, ko uba, ko 'yar uwa, ko miji, ko mata, ko abokin wani da suka mutu suka bari," in ji Tor Wennesland wakilin MDD kan zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.

    Ana alhinin ne ta hanyar sassauto da tutar MDD ƙasa-ƙasa a hedikwatarta da ke birnin New York, da Birnin Ƙudus, da kuma faɗin duniya.

    Wannan ne adadi mafi yawa na ma'aikatan MDD da aka kashe a wani yaƙi a tariihi.

    Akasarin mutanen da aka kashe ma'aikatan agaji ne da ke aiki da hukumomin MDD daban-daban a Gaza, waɗanda da yawansu yanzu sun rufe aiki saboda ƙazancewar hare-haren da Isra'ila ke kaiwa.

    Ma'aikatar lafiya a Gaza ta ce zuwa yanzu Isra'ila ta kashe sama da Falasɗinawa 11,000 a hare-haren da ta ƙaddamar bayan harin da Hamas ta kai cikin ƙasar ranar 7 ga watan Oktoba.

  10. Zaɓen Bayelsa: Sakamakon ƙaramar hukumar Brass

    Masu katin zaɓe: 94040

    Masu katin da aka tantance: 32064

    APC: 18431

    LP: 83

    PDP: 12602

    Jimillar ƙuri'un da aka kaɗa: 31614

    Halastattun ƙuri'u: 31211

    Ƙuri'un da aka soke: 403

  11. Inec ta ci gaba da zaman tattara sakamakon zaɓen Bayelsa

    Hukumar zaɓen Najeriya a jihar Bayelsa da ke kudancin ƙasar ta ci gaba da zaman tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar.

    Sakamakon ƙaramar hukuma biyu ne suka rage, Kudancin Ijaw da kuma Nembe, waɗanda aka ɗage su zuwa yau Litinin.

    Bayelsa na da ƙananan hukumomi takwas, kuma tuni aka sanar da shida daga cikinsu, inda Gwamna Douye Diri na jam'iyar PDP ke kan gaba da ƙuri'a 137,909, da kuma Timipre Sylva na APC mai 73,503.

    Tun a jiya Lahadi APC ta bayyana fargaba game da yunƙurin da ta ce Inec ta yi na mayar da tattara sakamakon zaɓen a Kudancin Ijaw da Brass zuwa Yenagoa babban birnin jihar, tana mai cewa tungarta ce.

  12. EU na neman tsahirtawa 'mai ma'ana' a yaƙin Isra'ila kan Gaza

    Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) ta nemi tsahirtawa "mai ma'ana" a yaƙin da Isra'ila ke yi a Zirin Gaza don kai agajin man fetur ga asibitoci.

    Janez Lenarcic, kwamishinan EU mai kula da rikice-rikice, ya faɗa yayin wata ganawa a birnin Brussels ranar Litinin cewa "sama da rabin asibitoci a Gaza sun daina aiki...kuma saboda ƙarancin man fetur ne".

    "Dole ne wanann tsahirtawa ta zama mai ma'ana," in ji shi.

    "Da farko dai, dole ne a sanar tun kafin lokacin ya zo saboda ƙungiyoyi su yi amfani da damar. Na biyu kuma, dole ne a fayyace tsawon lokacin da za ta ɗauka."

    Isra'ila ba ta bari an shigar da man fetur ba tun bayan hare-haren da ta fara kaiwa a ranar 7 ga watan Oktoba.

    A ranar Lahadi mambobin ƙungiyar ta EU 27 suka fitar da sanarwar neman "tsahirta yaƙi nan take" da kuma yin tir da Hamas kan abin da suka yi iƙirari cewa tana yin amfani da asibitoci da fararen hula a matsayin "garkuwa".

  13. Labarai da dumi-dumi, An naɗa tsohon firaminista David Cameron sakataren harkokin wajen Birtaniya

    Fadar Downing Street ta Birtaniya ta sanar da naɗa tsohon firaministan ƙasar David Cameron a matsayin sakataren harkokin waje na ƙasar.

    Mista Cameron ya maye gurbin James Cleverly ne, wanda shi kuma ya maye gurbin Suella Braverman a matsayin sakataren harkokin cikin gida.

    A safiyar Litinin ɗin nan aka kori Mrs Braverman daga muƙaminta bayan ta rubuta wata maƙala da ta saɓa wa manufar fadar gwamnatin kan zargin 'yan sanda da nuna son-kai a zanga-zangar nuna goyon bayan Falasɗinawa.

  14. An rufe titin jirgi a Abuja bayan jirgin sama ya yi saukar gaggawa

    An rufe ɗaya daga cikin titunan jirgin na filin jirgin sama na Abuja bayan wani jirgin fasinja mallakin Aerocontractors Airlines ya yi saukar gaggawa ranar Lahadi da safe.

    Rahotonni sun ce lamarin ya faru ne da jirgi samfurin Boeing 737 mai rajista 5N-BYQ.

    Sai dai an ci gaba da ayyuka kamar yadda aka saba 'yan awanni bayan janye jirgin da ya maƙale.

    Jirgin wanda ya taso daga Legas, ya yi yunƙurin sauka daga kan titin A4 ne lokacin da tayarsa ta gaba ta maƙale a cikin ciyayin da ke gefen titin.

    "Daga baya an rufe titin har sai da aka janye jirgin," in ji hukumar kula da lafiyar jirage ta Najeriya cikin wata sanarwa, tana mai cewa an ƙaddamar da bincike.

    "Babu wanda ya rasa rai ko jin rauni," a cewar James Odaudu cikin sanarwar.

  15. An kori sakatariyar harkokin cikin gida ta Birtaniya daga muƙaminta

    Firaministan Birtaniya ya kori Suella Braverman daga muƙaminta na sakatariyar harkokin cikin gida game da wata maƙala da ta saɓa wa fadar gwamnatin kan zargin 'yan sanda da nuna son-kai a harkar zanga-zanga.

    An zargi Mrs Braverman da ingiza tashin hankali a maƙalar da ta rubuta gabanin gudanar da zanga-zangar nuna goyon bayan Falasɗinawa a Landan a ƙarshen mako, inda aka yi arangama tsakanin masu macin da 'yan sanda.

    An kore ta ne da safiyar Litinin ɗin nan, kamar yadda wata majiya ta shaida wa BBC. Ba a bayyana sunan wanda zai maye gurbinta ba tukunna.

    An ga Sakataren Harkokin Waje James Cleverly na shiga Fadar Downing Street a safiyar Litinin kuma ana raɗe-raɗin cewa shi ne zai maye gurbinta a matsayin sakataren harkokin cikin gida.

    Haka nan, an ga tsohon firaminista David Cameron ma ya shiga fadar, abin da ya sa ake zaton zai koma gwamnati a matsayin sakataren harkokin waje.

  16. Zaɓen Kogi: Ba zan je kotu ba saboda ɓata lokaci ne - Ɗan takarar SDP Murtala Ajaka

    Ɗan takarar jam'iyyar Social Democratic Party (SDP) a zaɓen gwamnan jihar Kogi ya yi zargin cewa an yi maguɗi a zaɓen na ranar Asabar, yana mai cewa ba zai je kotu ba "saboda ɓata lokaci ne".

    Murtala Ajaka wanda ya zo na biyu a sakamakon da hukumar zaɓe Inec ta bayyana, ya faɗa wa kafar talabijin ta Channels TV cewa zuwa kotu ɓata lokaci ne "saboda hukumar zaɓen za ta je kotun kuma ta kare sakamakon da ta bayyana".

    Inec ta ce Usman Ododo na jam'iyyar APC ne ya yi nasara bayan ya samu ƙuri'a 446,237, sai Ajaka da ya samu 259,052, da kuma Dino Melaye na PDP mai ƙuri'a 46,362.

    "Na shafe shekara 20 ina siyasa, saboda haka na san yadda lamarin yake. Me zan je kotu na yi bayan Inec ɗin da suka yi wannan abin za su je kotun a matsayin waɗanda ake ƙara kuma su kare abin da suka aikata?" in ji Ajaka.

    "Wannan ɓata lokaci ne kawai, sai dai jam'iyya [ta kai ƙara] amma ni kam raina ya ɓaci sosai."

    Tun kafin a kammala tattara sakamakon zaɓen, ɗan takarar PDP Sanata Dino Melaye ya yi watsi da shi, yana mai neman Inec ta soke shi gaba ɗaya.

    • Sakamakon zaɓen gwamnan jihar Kogi da Imo da Bayelsa
  17. Yadda ruwan wutar Isra'ila ke haska samaniyar Gaza

    An tafka ƙazamin yaƙi a Zirin Gaza cikin dare yayin da Isra'ila ke ci gaba da ruwan wuta a zirin tsawon mako shida ta sama da ƙasa.

    A cikin wannan bidiyon na sama, wutar da ke tashi sakamakon harin da jiragen yaƙin Isra'ila ke kaiwa ta haska sararin samaniyar Gaza tare da balbalin hayaƙi da ya tashi.

    Ana ganin hasken wutar ne sosai saboda babu wuta a yankin arewacin Gaza gaba ɗaya, yayin da mazauna yankin da yawa suka yi hijira zuwa kudancin birnin bayan Isra'ila ta umarce su da su yi hakan.

  18. 'Yan fashin daji sun kashe 'yan sa-kai shida a jihar Zamfara

    Wasu 'yan fashin daji sun kai hari a yankin ƙaramar hukumar Bunguɗu da ke jihar Zamfara a arewacin Najeriya, inda suka kashe mutum takwas tare da raunata wasu da dama.

    Mazauna yankin sun ce 'yan bindigar sun kuma kwashi dukiyar jama’a mai tarin yawa da ta haɗa da dabbobi a harin da suka kai kan garin Gada ranar Juma'a da dare.

    Wani mazaunin yankin ya ce akwai mutum kusan bakwai da suka kai asibiti sakamakon raunukan da suka ji.

    Rundunar 'yan sandan Najeriya reshen Zamfara ta tabbatar wa da BBC Hausa cewa maharan sun kashe mayaƙan sa-kai shida lokacin da suka yi yunƙurin tare su bayan sun kai hare-haren.

    "Allah ya ba mu sa'a mun kashe 'yan fashin da dama kuma wasunsu sun gudu da raunuka," in ji ASP Yazid Abubakar kakakin rundunar a Zamfara.

    A jihar Katsina mai maƙwabtaka kuma, rundunar 'yan sandan jihar ta ce ta kashe wani ƙasurgumin ɗan fashin daji a yankin Faskari.

  19. Amurka ta kai hare-hare cikin Syria

    Amurka ta ce ta kai hare-hare ta sama a wuri biyu da ke gabashin Syria masu alaƙa da mayaƙan juyin juya-halin Iran.

    Amurkar ta ce wannan hari ɓangare ne na samamen da ake ci gaba da kaiwa kan sansanin sojinta da ke Syria.

    Sakataren Tsaron Amurka Lloyd Austin ya ce sun kai harin ne a kusa da biranen Abu Kamal da Mayadin.

    Ya ƙara da cewa Shugaba Biden ne ya ba da umarnin kai hare-haren domin tabbatar da cewa "Amurka za ta yi duk mai yiwuwa game da kare tsaronta da na ƙasarta baki ɗaya".

  20. Barka

    Maraba da sake haɗuwa a shafin labarai kai-tsaye, wanda zai kawo rahotonni kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa daga sassan duniya.

    Umar Mikail ne ke fatan mun hantsanta lafiya.