Dangin mutanen da Hamas ke garkuwa da su na neman ganawa da gwamnatin yaƙi ta Isra'ila
'Yan uwan Isra'ilawan da ƙungiyar Hamas ke garkuwa da su a Gaza sun ce sun shafe dare cikin "babbar zaƙuwa" sakamakon hare-haren da rundunar sojin Isra'ila ta tsananta a kan Zirin na Gaza.
Cikin wata sanarwa a safiyar yau, 'yan uwan mutanen sun nemi ministan tsaron Isra'ila da mambobin majalisar yaƙi ta ƙasar su gana da su cikin gaggawa.
"Daraen da ya gabata ya zama mafi muni a wajenmu. Ba mu iya barci ba tsawon dare saboda munanan hare-hare a kan Gaza, abin da ya sa muke fargaba game da halin da mutanen da ake riƙe da su ke ciki, waɗanda harin zai iya shafa," a cewar sanarwar.
Sanarwar ta ƙara da cewa kai hari ta ƙasa zai saka rayuwar tsararrun cikin haɗari.