Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Zaɓen 2023: Atiku da Peter Obi za su ɗaukaka ƙara zuwa kotun ƙoli

Wannan shafin yana kawo muku labarai kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza, Mukhtar Adamu Bawa and Umar Mikail

  1. Amurka ta sanya wa wani babban jami'in RSF na Sudan takunkumi

    Amurka ta ƙaƙaba wa wani babban jami'in rundunar mayaƙan RSF na Sudan takunkumi sakamakon rikicin ƙasar.

    An sanya wa Abdelrahim Dagalo, mataimakin shugaban rundunar takunkumi kan cin zarafin ɗan'adam a lokacin yaƙin da rundunar ke yi da sojojin Sudan.

    Amurka ta sanar da matakin ne ranar Laraba, a wani martani da ta yi kan mummunan rikici da aka samu a yankin Darfur da ke yammacin ƙasar, inda aka zargi RSF da haɗa kai da ƙungiyar 'yan tayar da ƙayar baya ta yankin.

    Amurka ta zargi Mista Dagalo da laifukan da suke da alaƙa da cin zarafin ɗan'adam, irin su "fyaɗe da kashe mutane saboda ƙabilarsu".

    Masu sanya ido kan yaƙe-yaƙe da ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama da shaidu na zargin RSF da hannu da rikicin yankin Darfur.

  2. Sojojin Gabon sun saki Ali Bongo

    Sojojin da suka yi juyin mulki a Gabon sun bayyana kawo ƙarshen ɗaurin talalar da suke yi wa hamɓararren shugaban ƙasar Ali Bongo, suna masu cewa a yanzu yana da damar barin ƙasar.

    Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin mulkin sojin, Kanal Ulrich Manfoumbi, sojojin suka karanta a gidan talbijin na ƙasar ranar Laraba da maraice, ya ce an saki Ali Bongo ne bisa dalilai na rashin lafiya.

    "A yanzu, idan ya ga dama yana iya fita daga ƙasar domin a duba lafiyarsa," in ji sanarwar.

    Tun bayan da sojojin suka kifar da gwamnatin Ali Bongo ranar 30 ga watan Agusta ne suka ci gaba da tsare a gidansa.

    Matakin sakin hamɓararren shugaban ƙasar na zuwa ne bayan da sojojin suke ta samun matsin lamba daga ƙungiyar ƙasashen tsakiyar Afirka da ECCAS da kuma maƙwabtan ƙasar na cewa su martaba lafiya tare da mutunta hamɓararren shugaban ƙasar

    A shekarar 2018 ne dai, Ali Bongo ya gamu da cutar shanyewar ɓarin jiki.

    Yanayin lafiyarsa ya kasance abin damuwa musamman a lokacin yaƙin neman zaɓe.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar shafin BBC Hausa kai-tsaye, kun wayi gari lafiya.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a wannan rana ta Alhamis, domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Kuna iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta da muhawara.