Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Zaɓen 2023: Atiku da Peter Obi za su ɗaukaka ƙara zuwa kotun ƙoli

Wannan shafin yana kawo muku labarai kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza, Mukhtar Adamu Bawa and Umar Mikail

  1. Mu kwana lafiya

    Masu bibiyarmu a wannan shafi, mun kawo ƙarshe a rahotannin da muke kawowa daga sassan duniya na yau Alhamis.

    Za mu kawo muku wasu gobe da safe idan Allah ya kai mu.

    Umar Mikail ne ke muku sallama tare da fatan za ku kasance da mu goben.

  2. Zaɓen 2023: Atiku da Peter Obi za su ɗaukaka ƙara zuwa kotun ƙoli

    Ɗan takarar jam'iyyar PDP Atiku Abubakar, da takwaransa na Labour Peter Obi a zaɓen shugaban ƙasar Najeriya na 2023 sun nemi lauyoyinsu su ɗaukaka ƙara kan hukuncin kotu da ya jaddada nasarar Bola Tinubu a zaɓen.

    Atiku ya ce ya je kotun ne bisa imanin samnun adalci. "A tarihin siyasata ina da yaƙini kan ɓangaren shari'ar ƙasarmu," in ji shi.

    "Tabbas ni ba baƙo ba ne a fannin shari'a, kuma zan iya cewa na san yadda tsarin ke aiki. Na daɗe ina gwagwarmaya a tsawon shekarun da na shafe a matsayin ɗan siyasa, kuma ina ganin zan iya dogara da ɓangaren shari'a wajen neman adalci."

    A nasa ɓangaren, Peter Obi, ya ce suna mutunta kotun, amma "ba zai taɓa sarewa wajen neman adalaci ga magoya bayansa ba".

    "A matsayinmu na masu ƙorafi, muna mutunta hukuncin kotun, amma ba mu yarda da hanyoyin da ta bi ba wajen yanke shi," in ji shi.

    "A matsayina na ɗan takara da kuma jam'iyyata Labour Party za mu ƙalubalanci wannan hukunci ta hanyar ɗaukaka ƙara nan take, kamar yadda tsarin mulki na Najeriya ya bayar da dama."

    A jiya Laraba alƙalan kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe ƙarƙashin Mai Shari'a Haruna Tsamani suka yi watsi da buƙatar Obi da Atiku sannan suka jaddada cewa Bola Tinubu na jam'iyyar APC ne ya lashe zaɓen na watan Fabrairu.

    • Dalili biyar na korar ƙararrakin Atiku da Obi
  3. Duniya ta gaza wajen tallafa wa mata - MDD

    Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta ce duniya na gazawa wajen agaza wa mata, kuma an gaza wajen cimma daidaito.

    Wani rahoto kan mata na MDD ya nuna cewa, ba a samu isasshen cigaba wajen kawo ƙarshen wariya da cin zarafi ba.

    Haka nan, samun haihuwa cikin yanayi mai kyau har yanzu ya kasance babbar matsala, kuma babu isassun mata a cikin harkokin siyasa da tattalin arziki.

    Rahoton ya kara da cewa ana bukatar karin kayan aiki don sauya yanayin da ake ciki a halin yanzu, kuma ya kamata mata su kasance cikin duk wasu shirye-shiryen kawo cigaba.

  4. Hankula sun tashi a Chadi bayan sojan Faransa ya kashe sojan ƙasar

    Masu zanga-zanga a ƙasar Chadi sun yi wa sansanin sojan Faransa ƙawanya cikin fushi bayan kashe sojan ƙasarsu.

    Rahotanni sun ce sojan na Chadi ya je sansanin Faya-Largeau da ke arewacin ƙasar don neman magani a ranar Talata.

    A cewar wasu majiyoyin Chadi da na Faransa, sojan ya kai wa wani ma'aikacin jinya hari da wuƙar tiyata.

    "Wani sojan Chadi da ba ya cikin hayyacinsa ya je sansanin Faransa don a saka masa bandeji, amma sai ya ɗauki wuƙa kuma ya ji wa wani soja ma'aikacin klafiya rauni," kamar yadda gwamnan yankin, Janar Ali Maide Kabir, ya faɗa wa AFP.

    "Ma'aikacin lafiyar ya yi amfani da bindigarsa kuma ya harbe sojan," a cewarsa.

    Wata majiya ta faɗa wa AFP cewa sojan ya ji wa ma'aikacin lafiyar rauni a maƙogaro da wuya da kuma kai.

    Sojojin na cikin waɗanda Faransa ta jibge a Chadi domin yaƙi da 'yan bindiga masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel.

    Lamarin ya fusata mazauna yankin, inda suka dinga zanga-zanga tare da yunƙurin shiga sansanin, amma sojojin Chadi sun hana su shiga.

  5. Kotu ta kama ɓarawon yara da laifi a Kenya

  6. Miji da mata sun ɓace bayan ambaliya ta share gidan shaƙatawarsu a Girka

    Wasu mata da miji 'yan Austria da suka je yawon shaƙatawa a Girka sun ɓace bayan ruwan sama mai ƙarfi ya yi awon gaba da gidan da suke ciki.

    Ma'aikatan gaji sun faɗa wa BBC cewa har yanzu suna ci gaba da neman ma'auratan da kuma wasu mutanen da suka ɓata.

    Ambaliyar ruwa ta tarfa mazauna tsakiyar ƙasar ta Girka a kan rufin gidajensu bayan ta cika kusan dukkan gidajen da ruwa.

    Zuwa yanzu an tabbatar da mutuwar mutum kusan 20 tun bayan da Guguwar Daneil ta afka wa Girka, da Turkiyya, da Bulgeriya a makon nan.

    Ma'auratan sun sauka a wani gida mai hawa ɗaya da suka kama don shaƙatawar yayin da ake shatata ruwa, kamar yadda mai gidan ya bayyana.

  7. Labarai da dumi-dumi, Zan ɗaukaka ƙara zuwa kotun ƙoli - Peter Obi

    Ɗan takarar jam'iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasar Najeriya na 2023, Peter Obi, ya nemi lauyoyinsa su ɗaukaka ƙara kan hukuncin kotu da ya jaddada nasarar Bola Tinubu a zaɓen.

    Da yake magana da manema labarai a birnin Onitsha na jihar Anambra, Mista Obi ya ce suna mutunta hukuncin kotun "amma ba shi ne na ƙarshe ba".

    "A matsayinmu na masu ƙorafi, muna mutunta hukuncin kotun, amma ba mu yarda da hanyoyin da ta bi ba wajen yanke shi," in ji shi.

    "A matsayina na ɗan takara da kuma jam'iyyata Labour Party za mu ƙalubalanci wannan hukunci ta hanyar ɗaukaka ƙara nan take, kamar yadda tsarin mulki na Najeriya ya bayar da dama.

    "Tuni tawagarmu ta lauyoyi ta samu umarnin ɗaukaka ƙarar. Ba zan taɓa sarewa ba wajen neman adalci, ba don kaina ba sai don dubban magoya bayanmu a faɗin ƙasa da wajenta."

    A jiya Laraba alƙalan kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe ƙarƙashin Mai Shari'a Haruna Tsamani suka yi watsi da buƙatar Obi da Atiku na jam'iyyar PDP, sannan suka jaddada cewa Bola Tinubu na jam'iyyar APC ne ya lashe zaɓen na watan Fabrairu.

  8. Sojojin mulkin Gabon sun naɗa Raymond Sima firaminista

    Sojojin mulkin Gabon sun naɗa Raymond Ndong Sima a matsayin firaminista na riƙon-ƙwarya.

    Mutumin mai shekara 68 masanin tattalin arziki ne kuma cikakken mai adawa da hamɓararren Shugaba Ali Bongo, duk da cewa ya yi aiki matsayin firaministan ƙasar daga 2012 zuwa 2014.

    Ya so ya shiga takarar shugaban ƙasa a zaɓen da aka kammala amma ya yanke shawarar mara wa babban ɗan takarar adawa Albert Ondo Ossa baya.

    Tun farko, sojojin mulkin sun ce sun saki Ali Bongo daga ɗaurin talalar da suka yi masa tun bayan da suka hamɓarar da gwamnatinsa.

    Janar Brice Oligui Nguema ne ya jagoranci juyin mulkin, wanda kuma aka rantsar a matsayin shugaban ƙasa na riƙon-ƙwarya ranar Litinin da ta wuce.

  9. Sheikh Giro ya gyara tarbiyyar al'umma a aikace da wa'azinsa - Buhari

    Tsohon Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya miƙa ta'aziyyarsa ga iyalan Sheikh Abubakar Giro Argungu sakamakon rasuwarsa bayan gajeriyar jinya ranar Laraba.

    "Ina miƙa ta'aziyyata ga iyalai da mabiyansa," in ji Buhari, yana mai addu'ar "Allah ya ji ƙan sa, ya saka shi cikin Jannatul-Firdaus".

    "Ya tsaya kan ɗabi'un Musulunci tare da nuna jajircewarsa a aikace wajen gyara tarbiyyar al'umma ta hanyar wa'azinsa da ayyukansa."

    A yau Alhamis aka yi jana'izar malamin a masallacin Idi na garin Argungu da ke jihar Kebbi, inda dubban mabiyansa suka halarci binne shi.

  10. Yadda aka gudanar da jana'izar Sheikh Giro Argungu

  11. Atiku zai ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙolin Najeriya

    Dan takarar shugaban Najeriya na jam'iyyar PDP Atiku Abubakar ya ce ya buƙaci lauyoyinsa su daukaka ƙara zuwa Kotun Koli.

    Yayin da yake jawabi a taron manema labarai da jam'iyyarsa ta shirya kan hukuncin kotun sauraron ƙorafin zaɓe, Atiku ya ce "faɗan bai ƙare ba".

    Atiku ya ce ya je kotun ne bisa imanin samnun adalci. "A tarihin siyasata ina da yaƙini kan ɓangaren shari'ar ƙasarmu," in ji shi.

    "Tabbas ni ba baƙo ba ne a fannin shari'a, kuma zan iya cewa na san yadda tsarin ke aiki. Na daɗe ina gwagwarmaya a tsawon shekarun da na shafe a matsayin ɗan siyasa, kuma ina ganin zan iya dogara da ɓangaren shari'a wajen neman adalci."

    A ranar Laraba ne kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen shugaban ƙasa ta yi watsi da ƙarar da Atiku da PDP da wasu jam'iyyun adawa suka shigar suna ƙalubalantar nasarar Shugaba Tinubu na APC.

  12. Jirgin sama ya juya yana tsaka da tafiya bayan fasinja ya ɓarke da gudawa

    Wani jirgin sama mallakin kamfanin sufuri na Delta da ke Amurka, wanda ke kan hanyarsa ta zuwa birnin Barcelona daga Atlanta ya juya ala-tilas bayan da wani fasinja ya ɓarke da gudawa.

    Tun farko dai jirgin ya kwashe awa biyu yana tafiya a sama, sa'ilin da matuƙin jirgin ya buƙaci sake juya akalar jirgin domin komawa inda ya taso.

    A cikin wata murya da aka wallafa a shafin X, an ji matuƙin jirgin na cewa wani fasinja "ya feshe cikin jirgin da gudawa."

    A wata sanarwa da ya fitar, kamfanin sufurin jiragen sama na Delta ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an samu wata matsala wadda ta sanya jirgin ya koma Atlanta domin a tsaftace shi.

    Sanarwar ta ce Jirgin Delta mai lamba 194 daga Atlanta zuwa Barcelona ya koma inda ya tashi bayan wani ya kamu da rashin lafiya lokacin da ake tsaka da tafiya.

    "Ma'aikatanmu sun yi aiki cikin gaggawa inda suka tsaftace jirgin tas, sannan aka kai fasinjoji zuwa inda suka nufa."

    Kamfanin ya nemi afuwar fasinjoji kan jinkirin da aka samu.

  13. Ƴan sandan Nijar sun koka kan ƙaruwar fyaɗe a wurin zanga-zanga

    Hukumar 'yan sandan jamhuriyar Nijar ta koka kan yadda ake yi wa 'yan mata fyaɗe a wajen zaman dirshen da ƙungiyoyin da ke adawa da zaman sojojin Faransa a Nijar ke ci gaba da yi.

    Babban daraktan hukumar 'yan sanda ta Yamai ne ya sanar da haka yayin ziyarar da ya kai wurin da fafaren hular ke zaman dirshen.

    Yayin da yake zantawa da manema labarai, daraktan 'yan sandan ya zayyano wasu muggan halaye kamar cin zarafi da wulakanta jama'a da kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa da masu zaman dirshen ɗin ke yi a kusa da babban titin shiga birnin Yamai.

    Latsa hoton ƙasa ku saurari rahoton Tchima Illa Issoufou daga Yamai:

  14. Dalili biyar na korar ƙararrakin Atiku da Obi

  15. Babu sauran adawa tsakanina da Messi - Ronaldo

    Fitaccen ɗan ƙwallon duniya Cristiano Ronaldo ya ce shi da babban abokin hamayyarsa a fagen ƙwallon ƙafa, Lionel Messi "sun sauya tarihin ƙwallon ƙafar duniya", to sai dai ya ce yanzu adawa tsakaninsu ta 'wuce'.

    'Yan wasan biyu - da ake yi wa laƙabi da, 'yan wasan da suka fi shahara a tarihi, 'GOAT' - sun sha fuskantar juna a lokacin da suke buga gasar La Liga a ƙungiyoyin Real Madrid da Barcelona.

    "Dukkanmu ana girmama mu a duniya, wannan shi ne babban abu mafi muhimmanci", in ji Ronaldo.

    Ronaldo - wanda ya lashe kyautar Ballon d'Or har sau biyar - a bana baya cikin mutanenda ke takarar kyautar karon farko tun 2003, yayin da Messi zai iya lashe kyautar karo takwas a tarihi.

  16. 'Yan sanda sun saki matar tsohon shugaban Zambiya

    'Yan sanda sun saki matar tsohon shugaban zambiya Edgar Lungu, jim kaɗan kamata tare da wasu mutum huɗu, kan zargin sace mota.

    Ana tuhumarsu da sace mota da takardar shaidar mallakar kadara a Lusaka babban birnin ƙasar, kamar yadda mai magana da yawun 'yan sandan Danny Mwale ya fitar.

    Ana kuma tuhumarsu da mallakar kadarorin da ake zargi na sata ne, zarge-zargen da duka suka musanta.

  17. Tinubu ya miƙa ta'aziyyarsa kan rasuwar Sheikh Giro Argungu

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya aike da ta'aziyyarsa ga iyalai da 'yan uwa da abokai da mabiyan fitaccen malamin addinin Musuluncin ƙasar Sheikh Abubakar Giro Argungu, wanda ya rasu ranar Laraba.

    Shugaba Tinubu ya bayyana mutuwar malamin da babban rashi ga ƙasar baki ɗaya, sakamakon irin gudunmowar da yake bayarwa wajen yaɗa ilimin addinin musulunci da gyaran tarbiyya ga ƙasar.

    "Za a daɗe ana tunawa da Sheikh Giro Argungu a ƙasarnan sakamakon shekarun da ya ɗauka yana yaɗa ilimin addini a ƙasar", in ji Tinubu, cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ya fitar.

    Ayyukan Malamin - ta hanyar ƙungiyar JIBWIS, inda ya kasance shugaban kwamitin gudanarwa na ƙungiyar - sun taimaka wajen ilimantar da matasan Musulmin ƙasar.

    Tinubu ya ce za a daɗe ana tuna malamin kan irin tsoron Allah da tawali'unsa da yadda yake kiran shugabanni a matakai daban-daban wajen sauke nauyin talakawa da ya rataya a wuyansu.

    Daga ƙarshe shugaban ya miƙa ta'aziyyarsa ga iyalai, da gwamnatin jihar Kebbi da musulman Najeriya, kan wannan babban rashi, tare da yin addu'ar samun gafara shehin malamin.

    • Tinubu ya nemi malamai su koma Nijar a karo na uku
  18. 'Zan saya wa Atiku awaki na mayar da shi gida ya yi kiwo'

    Ana ci gaba da mayar da martani a Najeriya kan hukuncin kotun sauraron ƙararrakin zaɓe na ranar Laraba, wanda ya bai wa Shugaba Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima nasara.

    Kotun dai ta kori buƙatar masu ƙorafi da ke neman soke cancantar zaɓen Bola Tinubu da mataimakin nasa.

    Kuma jim kaɗan bayan fitowa daga kotun, mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima wanda ya halarci zaman kotun na tsawon wunin rana, ya yi kira ga masu ƙorafin da cewa su zo su mara baya ga gwamnatinsu don yin tafiya tare da nufin ciyar da al'ummar Najeriya gaba.

    A cewarsa, lokacin siyasa ya wuce, kamata ya yi 'yan adawar su ba da dama ga gwamnati ta mayar da hankali wajen sauke nauyin da 'yan Najeriya suka ɗora mata na kawo sauƙi a rayuwarsu, musamman a wannan lokaci na matsin rayuwa.

    Sai dai, Kashim Shettima ya yi amfani da wannan damar wajen yin wasansu na Fulani da Bare-bari, inda ya ce zai saya wa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar awaki, ya mayar da shi garinsu, ya je ya yi kiwo.

    Shettima ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai jim kaɗan bayan yanke hukuncin kotun ƙararraƙin zaɓen shugaban ƙasar ranar Laraba.

    Bayan ya yi kira ga abokan hamayyarsa a siyance da su haɗa hannu wajen ciyar da Najeriya gaba, ɗaya daga cikin 'yan jarida ya tambaye shi ko zai yi wa Atiku ritaya a siyasance kamar yadda ya taɓa ambatawa a lokacin yaƙin neman zaɓe?

    "A yanzu mun shiga lokacin mulki, mun wuce batun zaɓe. Atiku Abubakar dattijon ƙasa ne da nake matuƙar girmamawa", in ji tsohon gwamnan na Borno.

    "Duk wanda ya san irin wasan barkwancin da ke tsakanin ƙabilar Fulani da ta Kanuri ya san cewa ina da damar tsokanarsa yadda na ga dama".

    “Don haka ba za mu mayar da Atiku Dubai ko Morocco ba, a maimakon haka zan mayar da shi Fombina, in saya masa awaki da kaji domin ya yi kiwo''.

    Duk da haka ya kuma ce: "Haƙiƙanin gaskiya, Atiku dattijon ƙasa ne. Najeriya tana buƙatarsa''.

    “Ƙwarewa ba abu ne da za ka sayo a kasuwa ba. Za mu ƙaru da ƙwarewarsa wajen gina ƙasarmu, siyasa ta ƙare yanzu maganar gwamnati ake yi".

    • Mene ne asalin wasan da ke tsakanin Barebari da Fulani?
    • Ina neman afuwar Musulmai kan kalamaina – Kashim Shettima
  19. Buhari ya yaba da hukuncin kotun ƙararrakin zaɓe

    Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana jin daɗinsa kan hukuncin da kotun ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasa ta yanke.

    Wanda ya tabbatar da nasarar jam'iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a watan Fabrairu.

    Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun tsohon shugaban ƙasar, Mallam Garba Shehu ya fitar, Buhari ya ce kotun ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasar ta "kafa tarihi" ta hanyar yin watsi da duk wata barazana da zarge-zarge marasa tushe wajen yanke hukunci cikin gaskiya da adalci, don martaba zaɓin 'yan Najeriya.

    Buhari ya ce "duk wanda ya yi nasara a yau dimokraɗiyya da al'umma ne suka yi nasara, idan Kotun Ƙoli ta yanke hukunci, to an gama da batun zaɓe lokaci ne da ya kamata ƙurar zaɓe ta kwanta".

    "Gwamnatin APC ƙarƙashin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ta samu goyon bayan kowa domin cika alƙawuran da ta ɗaukar wa al'umma", in ji Buhari.

    Toshon shugaban ƙasar ya kuma aike da saƙon taya murna ga shugaban ƙasar Bola Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima da kuma jam'iyyar APC kan wanna nasara da suka samu a kotu.

    • Tinubu ya kai wa Buhari ziyara bayan lashe zaɓe
    • Ganduje ya taya Tinubu murnar lashe zaɓe
  20. 'Najeriya ta yi asarar dala biliyan 100 saboda rikici a arewa maso gabashin ƙasar'

    Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya Unicef ya ce Najeriya ta yi asarar dala biliyan 100 sakamakon yaƙin da ake yi a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

    Cikin wani sabon bincike da Asusun ya gudanar ya yi gargaɗin cewa lokaci ya yi da muhukunta za su ɗauki mataki, saboda yadda rayuwar ƙananan yara ke cikin barazana.

    Binciken ya ce kusan yara miliyan ɗaya ne ba sa zuwa makaranta a yankin sakamakon rikicin 'yan bindiga da yankin ke fama da shi.

    Unicef ya kuma nuna yadda rikicin ya ƙara ta'azzara tattalin arzikin ƙasar, lamarin da asusun ya ce na barazana ga rayuwar miliyoyin ƙananan yara ga ƙasar baki-ɗaya.

    "Illar yaƙi ba ta tsayawa ga yankin da ake gwabza yaƙin kaɗai ba. Duka Najeriya na ji a jikinta sakamakon yakin da ake yi a yankin, tattalin arzikinta ya samu cikas sakamkon wanna rikici", in ji rahoton binciken.