Kotun sauraraon ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya ta fara ɗaukar hamara gabanin yanke hukunci kan ƙorafe-ƙorafen zaɓe da jam'iyyun adawa suka shigar gabanta.
Jam'iyyun PDP da LP ne suka shigara da ƙara suna ƙalaubalantar nasarar da Bola Tinibu na APC ya samu a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar cikin watan Fabrairun wanna shekara.
Tuni wakilan jam'iyyu suka fara isa kotun domin sauraraon hukuncin da kotun za ta sanar.
Daga ɓangaren wadanda ake ƙara tuni mataimakin shugaban ƙasar Sanata kashim Shettima da shugaban jam'iyyar APC na ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da gwamnan Yobe Mai Mala Buni da gwamnan Kogi Yahaya Bello.
Sai gwamnan Nasarawa Abdullahi A Sule da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkar tsaro Malam Nuhu Ridadu da shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa Femi Gbajabiamila da wasu kusoshin jam'iyya mai mulki suka isa kotun.
A ɓangaren jam'iyyar adawa tuni shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa Amb. Umar Illiya Damagun da gwamnan Bauchi sanata Bala Muhammad na PDP da wasu manyan kusoshin jam'iyyar suka hallara.
A ɓangaren jam'iyyar LP mai magana da yawun jam'iyyar Dakta Yunusa Tanko shi ma ya hallara a harabar kotu.
Ana sa ran 'yan takarar jam'iyyun adawa Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na jam'iyyar LP za su halarci zaman ktoun don jin irin hukuncin da kotun za ta yanke.
Bayan kammala zaɓen shugabna ƙasar ne dai jam'iyyun adawar suka shigar da ƙarar suna ƙalubalantar nasarar da hukumar zaɓen ƙasar INEC ta ce Bola Tnubu na APC ya samu.
Kotun wadda ke zamanta a Abuja, za ta sanar da hukunci kan ƙararrakin da wasu 'yan takara a zaɓen 25 ga watan Fabrairun 2023, suka shigar gabanta.
Atiku Abubakar, jagoran adawa a Najeriya, da Mista Peter Obi, ɗan takarar da ya zo na uku da kuma jam'iyyar APM, duka suna ja da kan sakamakon da ya bai wa Bola Tinubu nasara a zaɓen.