Jakadan Sudan ya roƙi ƴan Najeriya su koma ƙasar idan ƙura ta lafa
Jakadan Sudan a Najeriya, Muhammad Yusuf, ya roki ‘yan Najeriya da ke dawowa daga ƙasar da ke fama da rikici da su yi hakuri su koma idan al’amura suka lafa.
Da yake magana a ranar Alhamis bayan dawowar wasu ‘yan Najeriya daga ƙasar, Mista Yusuf ya bukace su da su koma karatu tare da buɗe sana’o’insu bayan an kawo karshen faɗan da ake yi tsakanin sojoji da dakarun RSF.
Ya bukace su da su ɗauki Sudan a matsayin kasarsu ta biyu, yana mai nuna ƙwarin gwiwar cewa za a shawo kan faɗan nan ba da daɗewa ba.
A yau Juma’a ne ake sa ran wasu ‘yan Najeriya da suka maƙale a Sudan ɗin za su koma gida.