Samar da ayyukan yi ba ya cikin haƙƙokin gwamnati – Adesina
Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin yaɗa labarai Femi Adesina ya ce samar da ayyukan yi ga 'yan ƙasa ba ya cikin haƙƙoƙin da suka rataya a wuyan gwamnati.
Mista Adesina ya bayyana hakan ne a shirin ‘The Morning Show’ na gidan talbijin din Arise TV, lokacin da yake magana game da nasarorin da gwamnatin Shugaba Buhari ta samu a cikin shekara takwas.
Adesina ya ce abin da kawai gwamnati za ta yi shi ne samar da kyakkyawan yanayi ga kamfanoni masu zaman kansu don su samar da ayyuka.
“Mafi yawan ayyukan da ake so ana samun su ne a kamfanoni masu zaman kansu. matuƙar aka samu kyakkyawan yanayi, kamfanoni masu zaman kansu ne za su samar da ayyukan yi''.
Mista Adesina ya kuma ce gwamnatin Buhari ta cimma nasarori a ɓangarori da dama da suka haɗar da ɓagaren mai da albarkatun iskar gas, da ayyukan more rayuwa da samar da dokoki da tsaro.