Afirka ta Kudu ta girke sojoji a asibitocin ƙasar kan yajin aikin ma'aikata
Afirka ta Kudu ta girke dakarun soji a asibitocin ƙasar yayin da ake ci gaba da samun ƙaruwar rahotonnin da ke cewa likitoci za su shiga yajin aikin da ma'aikata ke yi a ƙasar kan ƙarin albashi.
Tun cikin makon da ya gabata ma'aikatan gwamnati a ƙasar ke zanga-zangar neman ƙarin kashi 10 cikin 100 na albashi. Gwamnatin ƙasar dai ta yi wa ma'aikatan karin kashi 4.7 cikin 100.
Ƙungiyoyin ƙwadogon ƙasar sun sha alwashin ci gaba da zanga-zangar har sai gwamnatin ƙasar ta biya musu buƙatunsu.
Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ce an girke dakarun soji a asibitocin Thelle Mogoerane, da Sebokeng a yankin Bheki Mlangeni, yankin da zanga-zangar ta fi ƙamari.
Ministan lafiyar ƙasar Joe Phaahla ya ce yajin-aikin ya yi sanadiyyar rasa rayuka