Kotun Ƙolin Najeriya ta ɗage zaman sauraren shari'ar da wasu
gwamnonin jihohin ƙasar suka shigar kan ci gaba da amfani da tsofaffin kuɗin
ƙasar na takardar naira 200 da 500 da 1,000.
Kotun ta ɗage zaman ne bayan da wasu jihohi guda tara suka bi
sahun gwamnonin jihohin Kaduna da Kogi da kuma Zamfara waɗanda suka shigar da
ƙarar tun da farko.
Jihohin da ke ɓangaren masu ƙarar bayan
guda ukun na farko su ne Kano da Katsina da Sokoto da Lagos da Ondo da Ogun da
Ekiti da Rivers.
Ita ma a ɓangarenta gwamnatin ƙasar ta samu
jihohin Edo da Bayelsa a matsayin waɗanda ke kare kai a shariar.
Gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai
da takwaransa na jihar Kogi Yahaya Bello sun halarci Kotun a yau.
Yanzu dai al’ummar Najeriya za su ci gaba
da jira har zuwa 22 ga watan Na Fabrairu kafin sanin matsaya game da ci gaba da
amfani da tsofaffin takardun kuɗin ko kuma a’a.
Gwamnatocin jihohin Kaduna, da Zamfa da
kuma Kogi ne suka shigar da ƙarar, inda tun farko kotun ta bayar da umurnin
jingine wa’adin daina amfani da takardun kuɗin na 10 ga watan Fabrairu, wanda
bankin ya bayar a farko.
Mutane dai a Najeriya sun shiga ruɗani a
kan ko za su iya ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin na naira 1,000,
da 500, da 200 duk da umurnin da kotu ta bayar na jingine wa’adin na 10 ga
watan Fabrairu.
Haka nan rahotanni daga wurare da dama sun
nuna cewa bankuna sun daina karɓar tsofaffin takardun kuɗin, suna bayar da
hujjar cewa umurni ne suka samu daga Babban Bankin na Najeriya.
Bugu da ƙari wasu masu ƙananan sana’o’in da
dama sun daina amsar tsofaffin kuɗaɗen.