Yarinyar da ta yi fada da kada don tsira da ranta a Mozambique
Wata yarinya 'yar kimanin shekara tara da haihuwa ta tsallake rijiya da baya bayan ta kaucewa harin wata kada a lardin Chibuto da ke kudancin Mozambique.
Yarinyar na yin ninkaya ne a wani kogi da ke Limpopo a lokacin da kadar ta far mata.
Ta shaida wa manema labari cewa a lokacin da ta fuskanci kadar ta kawo mata hari sai ta yi kokari ta karci hancinta wanda a yayin hakan ne ta samu mummunan rauni a daya daga kafafunta.
Ta ce," Sai da kadar ta ja ni da karfi ta rike ni, ni kuma sai na yi kokari na kai mata duka sannan na karci hancinta,a nan ne da ta ji zafin duka ta sake ni ta wullar dani gefe."
A yanzu yarinyar na asibiti inda ake kula da ita kuma tana samun sauki.
Wani likita a asibitin da aka kai yarinyar ya ce wannan ne karo na biyu a cikin shekara guda da aka kai musu marar lafiyar da kada ta jiwa rauni.
Harin kada a Mozambique ba wani sabon abu bane.