Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC a Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya yi alwashin magance matsalolin da ke damun
kasar idan ya samu nasarar karbar mulki a babban zaben da ke tafe.
A yau ne dan
takarar ya kaddamar da yakin neman zaben nasa a Jos, babban birnin jihar
Filato, wanda Shugaba Buhari da sauran jiga-jigan jam’iyyar suka
halarta.
Mista Bola Tinubu
ya lissafa mafi yawan matsalolin da ke damun Najeriya, ciki har da ƙarancin
abubuwan more rayuwa, da durƙushewar masana’antu, da rashin aikin yi a tsakanin matasa.
Kana ya yi
alwashin magance su ta hanyar haɗa ƙwararru kuma gogaggu a cikin gwamnatinsa idan
ya samu nasarar kafawa.
“Mu a jam’iyyar
APC, wato Tinubu da Shetima da yardar Allah mun yi wa ƴan Najeriya alkawarin
yin shugabanci nagari a karakashin wannan yunƙuri na farfadowa ko sabunta fatan
alheri a zuƙatan al’umma, sakamakon goyon bayan da kuke ba mu. Za mu hada
ayarin jarumai don ciyar da kasa gaba.”
Kazalika, dan
takarar shugaban kasar ya caccaki abokan hamayyarsa… musamman ma na jam’iyyun
adawa da ke gaba-gaba, wani lokaci har da kiran suna yana gugar-zana, yana cewa
ba su san hanya ba, ballantana su yi wa wani jagora.
Shi ma abokin
takararsa, wato tsohon gwamnan jihar Borno, Sanata Kashim Shetima da ya hau
dandamali, bai ragar wa abokan hamyayyar nasu ba, yana cewa idan ka ji mutum ya
ce zai ba ka riga to ka dubi ta wuyansa.
Duk da cewa Shugaba
Muhammadu Buhari ya halarci wajen taron amma bai ce komai ba, face danƙawa ɗan
takarar tutar jam’iyya da ya yi.
Sai dai daya daga
cikin gwamnonin da suka yi jawabi, Gwamna Nasiru ElRufai na jihar Kaduna, ya mayar
da raddi ga masu kushe dan takarar yana cewa shi ne zabin manya.
Da dama da suka
yi jawabi sun nuna suna da kwarin gwiwa APC za ta kai labari a zabe mai zuwa.
Amma Shugaban jam’iyyar
APC na kasa Sanata Abdullahi Adamu ya shawarci ƴan jam’iyyar da ka da su
shagala, su bari mulki ya ruɗe su, su yi wa jam’iyya aiki idan suna so su ga
alheri.
“Kasancewa a kan
karagar mulki ba ya sa a dauwama a kan mulki. Ba zai hana faduwa ba idan ba mu
dage mun yi abin da ya kamata mu yi da zai ma samu karbuwa a zukatan masu kaɗa ƙuri’a
ba.
“Wannan ne ya sa nake jaddada cewa mu kasance masu himma.
Mu hada kai ta yadda za mu gudu tare mu tsira tare.”
An dai kammala
taro ana ta annashuwa, amma wani suɓul-da-baka da dan takarar
shugaban kasar ya yi ta janyo ce-ce-ku-ce, lokacin da zai yi fatan alheri ga jam’iyyar a karshen jawabinsa sai ya ɓuge da
ambaton sunan jam’iyyar adawa!
Sai dai nan take
ya gyara.