Zinace-zinace na haifar da yawaitar mutuwar aure a Zambia

Asalin hoton, Getty Images
Matsalar mutuwar aure a lardin gabashin Zambia na ƙaruwa cikin shekara biyu a jere, kamar yadda jaridar Zambia Daily taruwaito.
Lardin shi ne cibiyar harkokin noma na ƙasar.
A watanni takwas da suka gabata kimanin ma'aurata 3,400 ne suka shigar da neman a raba aurensu, a lardin.
Kuma akasarin waɗanda suka shigar da buƙatar kashe auren sun kafa hujja ne da zargin zina a ɓangaren mijin ko kuma matar.
A bara an samu mutuwar aure 4,441 ne, amma an yi hasashen cewar mace-macen auren na bana zai zarta na shekarar da ta gabata.
Sauran dalilan da ke haifar da mutuwar auren sun haɗa da cin zarafin abokin zama da kuma zaluntar juna.
Jaridar ta ce a kashe aurarraki da dama a yankin domin kauce wa cin zarafin juna da ke iya kai wa ga kisan kai.


















