Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

An fara ƙirga ƙuri'u a zaɓen gwamnan Jihar Ekiti

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita and Umar Mikail

  1. Sai da safenku

    Nan za mu rufe wannan shafi mai kawo rahotanni kai-tsaye.

    Za mu kawo yadda ta kasance a zaɓen gwamnan na Ekiti a wani shafin daban da zarar mun samu. Za ku iya bin sakamakon zaɓen a wannan shafin: Sakamakon zaben gwamnan Jihar Ekiti kai-tsaye

    Umar Mikail ne ke cewa mu zama lafiya.

  2. Za a fara diban alhazan Sokoto daga gobe Lahadi

    Jihar Sokoto ta ce za ta fara diban alhazanta zuwa aikin hajjin bana daga gobe Lahadi.

    Babban sakataren hukumar kula da jin dadin alhazai a jihar, Shehu Muhammad Dange, shi ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a yau Asabar.

    Shehu Muhammad ya ce jihar na da adadin maniyyata 2,404.

    Ya ce tuni hukumar ta samar wa alhazai 1,000 biza da kuma kudaden alawus. Ya kara da cewa an yi wa dukkan alhazan jihar allurar rigakafin korona.

    Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya nada kakakin majalisar dokokin jihar a matsayin shugaban tawagar alhazan a aikin hajjin na bana.

  3. Ta yaya dan takara zai yi nasara a zaben gwamnan Ekiti?

    Hukumar zabe mai zaman kanta da ke gudanar da zaben, ita ce zata sanar da wanda ya yi nasara a zaben gwamnan jihar Ekiti.

    A cewar hukumar, za a sanar da wanda yayi nasara a zaben gwamnan jihar Ekiti ne kawai, idan dan takara ya samu:

    • Yawan Kuri'un da aka kada a zaben; da kuma
    • Kar dan takara ya gaza samun kashi daya bisa hudu na dukkan kuri'un da aka kada a akalla kashi biyu bisa uku na dukkan kananan hukumomin jihar.
  4. Manyan 'yan takarar gwamna a zaɓen Ekiti

    An rufe rumfunan zaɓe da dama a yau Asabar bayan jefa ƙuri'u a zaɓen gwamnan jihar Ekiti na 2022.

    Duk wanda ya yi nasara a zaɓen zai maye gurbin gwamna mai barin gado Kayode Fayemi na jam'iyyar APC, wanda a cikin shekarar nan wa'adin mulkinsa zai ƙare.

    Tun a watan Janairu ne jam'iyyu suka gudanar da zaɓukan fitar da gwanayensu, kuma sunayen waɗanda hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasar INEC ta tantance ne kawai za su kasance a kan ƙuri'ar zaɓen.

    Ga dai bayanan wasu ƴan takarar da INEC ɗin ta tantance. An zaɓe su ne bisa waɗanda BBC ta iya samun su ko bayanansu a intanet, ba don wani ya fi wani ba.

    • BIODUN ABAYOMI OYEBANJI - APC
    • BISI KOLAWOLE - PDP
    • OLUSEGUN ONI - SDP
    • ADEBOWALE RANTI AJAYI - YPP
  5. Matakan da ake bi wajen tattara sakamakon zaɓen Ekiti

    Mataki na gaba da za a shiga a zaɓen gwamnan Jihar Ekiti bayan kammala kaɗa ƙuri'a da kuma ƙirga su a wasu rumfunan zaɓe shi ne tattara sakamakon.

    Tattara sakamakon na nufin haɗa kan lissafin adadin ƙuri'un da aka samu a rumfunan zaɓen tare da haɗa su wuri guda.

    Kowane ɓangare na da turawan zaɓe da INEC ta naɗa da za su gudanar da shi. Su ne kamar haka:

    • Baturen zaɓe na rumfar zaɓe zai tura sakamakon zaɓen zuwa wurin tattara sakamako na mazaɓa
    • Shi kum jami'in tattara sakamako zai karɓa ya aika matattarar sakamako ta ƙaramar hukuma
    • Jami'in tattara sakamako na ƙaramar hukuma zai aika wa baturen zaɓe na jiha
    • Shi kuma baturen zaɓe na jiha zai tattara sakamakon daga ƙananan hukumomi kuma ya sanar da su, sannan ya bayyana wanda ya yi nasara a zaɓen gwamnan
    • 'Yan talkara 16 ne ke fafatawa a zaɓen
  6. Abin da muke yi don inganta lantarki a Abuja - AEDC

    Kamfanin rarraba wutar lantarki a Najeriya da ke bai wa yankunan Abuja da jihohin Nasarawa da Kogi wuta ya nemi afuwar kwastomminsa, yana mai bayyana matakan da yake ɗauka wajen inganta samar da lantarkin.

    Cikin wata sanarwa da babban daraktan kamfanin, Adeoye Fadeyibi, ya fitar a yau Asabar ta ce kamfanin na Abuja Elecricity Distrubution Company (AEDC) ya ƙaddamar da wasu shirye-shirye don haɓaka samar da wutar.

    A cewar Mista Fadeyibi, AEDC zai sayo wasu sabbin na'urorin raba wuta 34 ta cikin shirin 40 Quick WIn Projects don rage yawan lodin da ke kan wasu na'urori a sassan Abuja.

    Kazalika, kamfanin ya ce zai duƙufa wajen gyara wasu na'urorin da suka kai 78 duka a cikin shirin.

    Najeriya na fama da ɗaukewar wutar lantarki a lokuta da dama a baya-bayan nan sakamakon lalacewar babban layin lantarki na ƙasa.

    Gwamnati kan zargi 'yan daba da lalata bututan iskar gas da ke bai wa tashoshin wutar makamashin aiki.

    • Mene ne babban layin wutar lantarki na Najeriya kuma yaya yake aiki?
  7. Gwamnan Zamfara Matawalle ya bai wa ma'aikata hutun mako ɗaya don su yi rajistar zaɓe

    Gwamnatin Jihar Zamfara a arewacin Najeriya ta bai wa ma'aikatan jihar hutun mako ɗaya domin su yi rajistar katin zaɓe da ake gudanarwa yanzu haka a faɗin ƙasar.

    Matakin na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamashinan Yaɗa Labarai na Zamfara Ibrahim Dosara ya fitar a yau Asabar.

    Ya ce Gwamna Bello Matawalle ya amince da ba da hutun ne daga Litinin, 20 zuwa 24 ga watan Yuni.

    "Sakamakon wannan sanarwa, an umarci dukkan kwamashinoni da masu bai wa gwamna shawara da sakatarori da sauran ma'aikatan gwamnati da jami'an jam'iyyun siyasa da su saka ido kan yadda aikin rajistar ke tafiya," a cewar kwamashinan.

    Ƙungiyoyi da 'yan gwagwarmaya a Najeriya na ci gaba da kira ga hukumar zaɓe ta ƙasa INEC da ta tsawaita wa'adin yin rajistar, suna masu cewa mutane da dama ba su samu damar yi ba saboda ƙarancin kayan aiki da kuma cunkoso.

    INEC ta saka ranar 30 ga watan Yuni a matsayin ranar ƙarshe da za a rufe aikin rajistar.

  8. An fara ƙirga ƙuri'u a zaɓen gwamnan Jihar Ekiti

    An fara ƙirga ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓen gwamnan Jihar Ekiti da ke kudancin Najeriya bayan kammala jefa ƙuri'un a yau Asabar.

    Tuni turawan zaɓe a rumfar zaɓe ta Irona 3 mazaɓa ta 11 suka fara ƙirga nasu ƙuri'un.

    Tun da misalin ƙarfe 2:30 aka kammala zaɓen a wasu rumfunan zaɓe, inda masu kaɗa ƙuri'a ke zaɓar ɗaya daga cikin 'yan takara 17 da ke fafatawa.

  9. An kammala kaɗa ƙuri'a a wasu rumfunan zaɓe a Ekiti

    An kammala kaɗa ƙuri'a a wasu daga cikin rumfunan zaɓe a Jihar Ekiti a zaɓen gwamnan jihar da ake gudanarwa a yau Asabar.

    A rumfar zaɓe mai lamba 39 da ke mazaɓa ta bakwai a Ado-Ekiti, tun 10:30 na safe aka kammala kaɗa ƙuri'a.

    Wasu daga cikin jami'an INEC sun shaida wa BBC cewa sai 2:30 na rana za su soma tantance ƙuri'un da aka jefa da kuma ƙirga su.

    Haka ma a Ƙananan Hukumomin Ikere da Irepodun-Ifelodun an kammala zaɓen da wuri.

  10. Jami'an EFCC sun yi awon gaba da wasu da ake zargi da sayen ƙuri'u a Ekiti

    Hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC ta kama wasu mutane da ake zargi da sayen ƙuri'u a yayin zaɓen gwamnan Ekiti.

    Tun da safiyar yau dama wasu daga cikin masu jefa ƙuri'a sun ta kokawa kan yadda suka ce ake sayen ƙuri'u a wasu rumfuna zaɓe.

    Wani bidiyo da gidan talabijin na Channels ya wallafa a shafinsa na Twitter ya nuna yadda jami'an EFCC suka yi dirar mikiya a wata rumfar zaɓe inda suka yi awon gaba da wasu.

  11. Ƴan sanda a Ekiti sun ce har yanzu babu wani rahoton tashin hankali yayin zaɓen

    Rundunar yan sandan Najeriya reshen Jihar Ekiti ta bayyana cewa zaɓen da ake gudanarwa a jihar zuwa yanzu babu wasu rahotanni da ke nuna cewa an samu tashin hankali.

    Mataimakin shugaban sufeton ƴan sandan Najeriya DIG Johnson Kokumo wanda shi ne ke jagorantar ɓangaren tsaro a zaɓen a jihar shi ya bayyana haka a yayin da yake jawabi ga jama'a a Ado-Ekiti.

  12. Wata mata mai shekara 90 ta kaɗa ƙuri'a a zaɓen Ekiti

    Wata mata mai shekara 90 mai suna Ashake Atogi ta kaɗa ƙuri'a a zaɓen Jihar Ekiti, kamar yadda hukumar INEC ta sanar a shafinta na Twitter.

    Ta kaɗa ƙuri'ar ne a rumfa mai lamba ɗaya da ke Irepodun/Ifelodun.

  13. Wasu na ƙorafi kan batun sayen ƙuri'a a zaɓen Ekiti

    Wasu daga cikin masu zaɓe a Ekiti sun harzuƙa kan wasu abubuwan da suke gani da ba su gane kansu ba.

    Masu zaɓen waɗanda akasarinsu mata ne sun yi zargin cewa ana sayen ƙuri'a.

    Wasu mata da ke rumfar zaɓe mai lamba 9 da 16 a mazaɓa ta 11 da ke Oke-ori omi sun ce suna so su yi zaɓe ne kawai ba sai an ba su kuɗi ba.

    "Su tafi da kuɗinsu. Ba mu so mu yi zabe saboda tukunyar miya ɗaya. "Suna biyan wasu N2,500 wasu kuma suna biyan 2,000," in ji ɗaya daga cikin masu zaɓen.

    Wasu daga cikin wakilan jam'iyyu sun koka kan cewa akwai wata jam'iyya da ke raba kuɗi kuma sun ƙi su ba waɗanda suka ƙi zaɓarsu kuɗin.

    "Muna so INEC ta turo sojoji waɗannan rumfunan zaben. Su kaɗai za su iya hana wannan sayen ƙuri'ar," in ji ɗaya daga cikin masu zaɓen.

  14. Ana ci gaba da kaɗa ƙuri'a a zaɓen Ekiti

    Ana dai ci gaba da gudanar da zaɓe a Jihar Ekiti domin zaɓen gwamnan da zai maye gurbin Kayode Fayemi.

    Hukumar INEC dai ta ce za a kammala kaɗa ƙuri'a da misalin 2:30 na rana.

    Zuwa yanzu dai babu wata matsala inda rahotanni ke cewa ana gudanar da zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana.

  15. Gwamnan Ekiti Kayode Fayemi ya kaɗa ƙuri'arsa

    Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi ya kaɗa ƙuri'arsa a zaben da ake gudanarwa a jihar.

    Mista Fayemi ya kaɗa ƙuri'ar tasa ne a rumfar zaɓensa da ke mazaɓa ta 11 a Isan-Ekiti. Ita ma matarsa ta kaɗa ƙuri'arta ba tare da wata matsala ba.

    Mista Fayemi ya yi kira ga waɗanda suka cancanci jefa ƙuri'a da su yi abin da ya dace wurin zaɓen wanda suke so ya jagorance su.

    Ya kuma buƙaci jama'a da su ba jami'an tsaro haɗin kai domin ganin an gudanar da zaɓen lafiya an kuma gama lafiya.

    Gwamna Fayemi dai zai miƙa ragamar jagorancin Jihar Ekiti ga duk wanda ya yi nasara a wannan zaɓe.

  16. Labarai da dumi-dumi, Ɗan takarar APC Biodun Oyebanji ya kaɗa ƙuri'arsa

    Ɗan takarar gwamna a Jihar Ekiti a ƙarƙashin jam'iyyar APC wato Biodun Oyebanji ya kaɗa ƙuri'arsa.

    Mista Biodun dai yana daga cikin manyan ƴan takara a Jihar.

  17. Labarai da dumi-dumi, Ɗan takarar Jam'iyyar SDP Segun Oni ya kaɗa ƙuri'arsa

    Ɗan takarar gwamna a Jihar Ekiti a ƙarƙashin Jam'iyyar SDP, Segun Oni ya kaɗa ƙuri'arsa.

    Ya kaɗa ƙuri'ar ne a mazaɓa ta biyu rumfa mai lamba huɗu a Ifaki Ekiti.

  18. Ƴan kasuwa na ci gaba da gudanar da kasuwancinsu a Ekiti

    A daidai lokacin da ake gudanar da zaɓe a Jihar Ekiti, wasu daga cikin ƴan kasuwa na ci gaba da gudanar da kasuwancinsu kamar yadda suka saba.

    Mata ƴan kasuwa sun taru a kasuwar Esa Oke da ke Ado-Ekiti domin gudanar da kasuwancinsu.

    "Wannan zaɓen da suke gudanarwa ba zai ba ni abinci ba. Idan ban sayar da wani abu yau ba, yarana za su ji yunwa," in ji wata ƴar kasuwa a yayin tattaunawa da BBC.

    Baya ga mata da ke sayar da kayayyaki a kasuwa, ana ci ga ba da gudanar da wasu sana'o'i a kan tituna.

    Akasarin masu sayar da kayayyaki a kan tituna abinci suke sayarwa ga masu zaɓe.

  19. Hotuna daga rumfunan zaɓen gwamna Ekiti

    Tuni dai aka soma kaɗa ƙuri'a a wasu sassa na Jihar Ekiti a zaɓen gwamnan jihar da ake gudanarwa.

    Duk da cewa a wasu wuraren mutane da dama sun fito rumfunan zaɓe, wasu wuraren kuwa mutane ƙalilan ne.

    Amma dai an soma tantance masu zaɓen da kuma kaɗa ƙuria a kusan duka rumfunan zaɓe kamar yadda hukumar INEC ta bayyana.

  20. Ana ci gaba da tantance masu zaɓe a Ekiti

    Jami'an hukumar zaɓe dai na ci gaba da tantance masu kaɗa ƙuri'a a Jihar Ekiti.

    Haka kuma bayan tantancewar masu zaɓen na dangwala ƙuri'a. An soma tantance masu zaɓe da kaɗa ƙuri'a a mazaɓa ta 10 rumfa mai lamba biyu da misalin 8:30 na safe haka ma a mazaɓa ta shida rumfa mai lamba shida