Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Yajin aiki: Dalibai sun rufe hanyoyin Ife-Ibadan, da Lagos-Abeokuta

Wannan shafi ne d ake kawo muku labarai da rahotanni na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

  1. Rufewa

    Anan muka kawp karshen wannan shafi na kai tsaye, da mu ke kawo muku labarai da rahotanni daga sassa daban-daban na duniya.

    Ku zarci shafinmu na intanet bbchausa.com, da shafukanmu na sada zumunta da muhawara na Facebook, da Instagram har da shafinmu na Youtube, domin kallon hotuna har da bidiyon shirye-shiryen da suka gaba da kuma sabbi.

    Muna fatan za ku kasance da mu a gobe idan Allah ya kai mu, a shirin Safe da misalin karfe 6:30, da shirin Hantsi da karfe 7:30, agogon Najeriya da Nijar.

    Badriyya Tijjani Kalarawi ke muku fatan alkhairi daga nan sashen Hausa na BBC.

    Mu kwana lafiya.

  2. Koriya ta Arewa:Mutum na farko mai korona ya janyo dokar kulle

    Hukumomi a Koriya ta Arewa sun bada umarnin sanya tsattsaurar dokar kulle, bayan samun mutum na farko da ya kamu da cutar korona.

    Kafar yada labaran kasar ta rawaito cewa, an samu bullar nau'in korona na Omicron a babban birnin kasar Pyongyang, sai dai ba a bayyana adadin wadanda suka kamu da cutar ta dalilin mutumin ba.

    Koriya ta Arewa dai ta yi watsi da dukkan nau'o'in allurar rigakafain cutar korona daga Hukumar Lafiya ta Duniya da sauran kasashe.

    Maimakon hakan, ta yi kokarin rufe iyakokin ta, kuma hukumomi ba su taba yin bayanin an samu wanda ya kamu da cutar ba, duk da cewa kwararru na cewa cutar ta dade da bulla a kasar.

    Wasu dai na cewa 'yan Koriya ta Arewa miliyan 25 na cikin tsaka mai wuya, sakamakon rashin amincewa da rigakafin da hukumomin kasar suka yi.

    Hatta wadda kasar China ta yi mai suna Sinovac, sam Koriya ta Arewa ta ki aminta da ita, a bangare guda kuma ana nuna fargaba kan raunin fannin kiwon lafiyar kasar.

  3. Sifaniya na duba yiwuwar bai wa matan da ke tsananin ciwon mara hutu

    Gwamnatin Sifaniya na shirin kaddamar da wata doka da za ta dinga bai wa mata masu fama da matsanancin ciwon mara lokacin da suke jinin Haila.

    Kafar yada labaran kasar ta bayyana cewa kudurin dokar zai tabbatr da mata sun samu hutun kwanaki uku zuwa biyar daga wuraren aiki.

    Sai dai 'yan siyasa na gargadi, daftarin kudurin da aka kwarmatawa kafafen yada labaran Sifaniya, ba a gama dubawa da karanta shi ba.

    Idan hakan ta tabbata, Sifaniya za ta zamo ta farko a kasashen Turai da za ta amince da hakan, duk da ya ke wasu tsirarun kasashe a duniya da suke da irin wannan doka.

    A dan tsakanin nan dai, majalisar dokokin Sifaniya na yin sauye-sauye da garanbawul a fannoni da dama da suka hada da fannin lafiya, da batun halasta zubda ciki da sauransu.

    A farkon wannan watan ne kafafen yada labaran kasar, suka samu ganin kwafin daftarin kudurin, wanda ake sa ran a mako mai zuwa za a yi masa karatu a zauren majalisa.

  4. Matar da aka zubawa Acid a Habasha na fuskantar barazana

    Wata mata 'yar kasar Habasha da aka zuwaba ruwan Acid a shekarar da ta gabata, ta ce maharan da aka yankewa daurin zaman kaso na kiran ta ta wayar tarhon daga jarun su na mata barazana.

    Selamawit Gizew, mai shekara 24, ta ce ta na jin tsoron abin da zai same ta, don haka ta koma gidan wasu 'yan uwansu saboda yadda wanda ya watsa mata acid din mai suna Yihenew Fenta ya na damun ta da waya.

    Sai dai shugaban 'yan sandan yankin, Birhanu Admasu ya ce maharin ba shi da wata hanya da zai samu wayar salula a kurkuku.

    'Yan uwan Selamawit sun ce, 'yan sanda ba sa wani taimaka musu bayan kai rahoton halin da 'yar su ke ciki a ranar da aka kai mata harin ranar 27 ga watan Disamba 2021, sun dauki wata guda kafin su gufanar da shi gaban kuliya.

    An dai yankewa Yihenew daurin shekara 14 a gidan kaso, bayan samun da laifin zubawa matashiyar ruwan Acid a fuskarta da wuya, kirjinta da kuma bayanta, a harin da matashin ya kai ma ta ta na fitowa daga kantin sai da magani da ta ke aiki a garin Keraniyo da ke yammacin kasar Habasha.

  5. Manjo na karshe mai hannu a kisan kare dangin Rwandan ya mutu

    An tabbatar da mutuwar tsohon jami'in gwamnatin Rwanda, da ake nema ruwa a jallo kan rawar daya taka a kisan kare dangin da aka yi a kasar a shekarar 1994.

    Protais Mpiranya ne ke jagorantar masu tsaron lafiyar shugaban kasa, kuma sama da shekaru 20 da suka gaba kotun da aka kafa a Rawanda ke nemansa.

    Bayan ya tsre, da kuma ake kyautata zayon ya na amfani da wani suna na daban, a karshe masu bincike sun gano kabarinsa a wajen birnin Harare na kasar Zimbabwe, inda aka ce a shekarar 2006 Mr Mpiranya ya rasu.

    Mai mukamin manjon soji na karshe da aka yankewa hukunci, karkashin kotun da aka kafa domin shari'ar yakin na Rwanda

    The last of the major fugitives indicted by the tribunal was accused of ordering the murders of senior moderate Rwandan leaders at the start of the genocide, including Prime Minister Agathe Uwilingiyimana.

    He was also charged with the murders of 10 Belgian UN peacekeepers.

  6. Shireen: Faladinawa za su kai batun kisan 'yar jaridar Al-j kotun ICC

    Shugaban Falasdinu ya ce ba tare da bata lokaci ba, zai shigar da batun kisan 'yar jaridar Al Jazeera Shireen Abu Aqla gaban kotun hukunta manyan laifuka ta duniya wato ICC.

    A wani jawabi da ya gabatar ga dubban 'yan kasar da suka halarci jana'izar ban girma da aka yi wa 'yar jaridar a birnin Ramallah, Mahmoud Abbas ya ce alhakin kisan ya rataya a wuyan Isra'ila.

    An harbi Abu Aqla a lokacin da ta ke bada rahoton samamen da Isra'ila ta kai yamma da gabar kogin Jordan.

    Kafar yada labaran Al Jazeera, ta ce sojin Isra'ila ne suka kashe Abu Aqla, ya yin da Isra'ila kuma ta ce 'yan bindigar Falasdinu ne suka harbe ta.

    A bangare guda kuma Majalisar Dinkin Duniya, da Amirka da Tarayyar Turai sun yi kiran a gudanar da bincike mai zaman kan shi kan kisan Abu Ala.

    Shireen Abu Aqla ta fara aiki da kafar yada labarai ta Al Jazeera shekaru 25 da suka gabata, wato shekara guda da bude fara watsa shirye-shiryensu a duniya.

    Tun daga lokacin ta ke bada rahoto kan abin da ya shafi Isra'ila da Falasdinu.

  7. Yajin aiki: Dalibai sun rufe hanyoyin Ife-Ibadan, da Lagos-Abeokuta

    A Najeriya wasu daliban jami'a sun yi zanga-zanga dauke da katon allon da aka rubuta “A kawo karshen yajin aikin ASUU,” daliban sun ce za su ci gaba da wannan bore har sai malaman jami'o'in kasar sun janye yajin aikin da suka tafi tare da sake bude jami'o'i domin ci gaba da karatu.

    Jaridar Premium Times ta rawaito cewa, daruruwan daliban ne suka rufe manyan hanyoyin da suka taso daga Ibadan da Elesa, da ke kusa da jami'ar Oduduwa.

    Wani bidiyo da Premium Times ta samu, daliban na cewa ba sa jin tsoron jami'an tsaro, tare da barazanar zaman dabaro a tituna har sai an bude jami'o'in.

    Sun bayyana takaicinsu kan yadda ake ci gaba da yajin aikin, sun kuma nuna takaici kan 'yan siyasa kan yadda sukai shakulatun bangaro da batunsu, ba sa taka rawar da ta dace wajen tabbatar da an biyawa malaman jami'o'in bukatunsu yadda za su koma daukar karatu.

    Maimakon hakan sun maida hankali kan sayan fom doin tsayawa takarar zabe a shekara mai zuwa, sun yi tamkar babu abin da ke faruwa.

    A farkon makon nan ne, kungiyar malaman jami'o'in ta Najeriya, ASUU, ta sanar da tsawaita wa'adin yajin aikin da suka tafi zuwa makwanni 12 sakamakon rashin cimma matsaya da gwamnati kan bukatunsu.

    ASUU ta shiga yajin aikin ne sakamakon abin da ta bayyana gazawar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari wajen aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla a baya game da yadda za a inganta harkokin karatun jami'a na kasar.

  8. Kotun Sri Lanka ta hana tsohon fira ministan kasar da wasu fita daga kasar

    Kotu a Sri Lanka ta hana tsohon Fira minista Mahinda Rajapaksa, da dansa da wasu na hannun damar sa 15 fita daga gasar.

    A ranar Litinin din data wuce ne Mr Rajapaksa, ya yi murabus biyo bayan mummunar zanga zangar kin jinin gwamnatinsa.

    Rahotanni sun ce an sake maido da dokar hana fita a fadin Sri Lanka, bayan daga wa al'umma kafa su fito su sayi kayan abinci.

    Bayan shafe makonni ana rikicin da ya yi sanadin mutuwar kusan mutun 10, a yanzu tituna sun kasance wayam, in banda dogayen layuka a gidajen mai.

  9. Kungiyoyin farar hula a Najeriya sun yi maraba da umarnin shugaban kasar na yin murabus din masu rike da mukami da ke son takara asar s

    Kungiyoyin farar hula a Najeriya sun yi maraba da umarnin da gwamnatin kasar ta bayar ga masu mukamai na nadi da ke sha`awar neman takara a zabe mai zuwa da su sauka daga mukamansu.

    Wannan umarnin da ya biyo bayan wani mai kama shi da shi wanda shugaba Buhari ya bayar.

    Umarnin ya fito ne daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Mista Boss Mustapha, wanda a cikin wata takardar da ya aika wa ma`aikatu da hukumomin gwamnati ya umurci shugabanni, wadanda ke rike da mukamai da nadi, ciki har da ministoci da jakadu da dai shugabannin hukumomi, wadanda kuma ke sha`awar neman takara a babban zaben da ke tafi da su hanzarta yin murabus daga mukaman nasu daga nan zuwa ranar Litinin mai zuwa, wato 16 ga wannan wata na Mayu.

    Sanarwar ta bukaci da su danka ragamar ma`aikatu ko hukumomin ga jam`ian da ke biye da su.

    Tun a jiya Laraba, shugaba Buhari ya ba da irin wannan umurnin bayan zaman majalisar zartarwar kasar.

    Gwamnatin Najeriyar ta dauki wannan matakin ne bayan kungiyoyin farar-hula sun caccake ta game da jinkirin yin hakan.

  10. MDD ta ce take hakkin bil adama da ake yi a Ukraine tamkar laifin yaki ne

    Shugabar hukumar kare hakkin dan adam ta Majalisar Dinkin Duniya Michelle Bachalet, ta ce an gano gawarwaki dubu guda a wasu yankuna na Kyiv, babban birnin Ukraine a 'yan makwannin nan.

    Hukumar na gudanar da bincike a kan zarge-zargen take hakkin dan adam din da aka yi tun bayan da Rasha ta fara mamaya a Ukraine.

    Shugabar hukumar ta ce, irin abubuwan da aka aikata da suka hada da kashe-kashe a yankunan arewacin Kyiv, abin tayar da hankali ne.

    Ta ce," Yayin da muke da bayanai a kan irin wadannan kashe-kashe 300, akwai yiwuwar adadin zai ci gaba da karuwa saboda sabbi shaidun da muke samu."

    Ta ci gaba da cewa,"Ana kashe fararen hula a lokacin da suke neman mafaka ko neman abinci da ruwan sha.

    A yayin da wasu kuma ake kashe su a lokacin da suke kokarin tserewa muhallansu a motoci saboda lugudan wutar Rasha.

  11. Har yanzu ba a ga mutum 48 ba bayan ambaliyar ruwan Afirka ta Kudu

    Mahukunta a Afirka ta Kudu sun tabbatar da cewa har yanzu akwai mutum 48 da ba a gani ba bayan mummunar ambaliyar ruwan da aka yi a KwaZulu-Natal.

    Mahukuntan sun ce ya zuwa yanzun mutum 445 ne aka tabbatar sun mutu sakamakon ambaliyar ruwan.

    Tagawar jami'an hukumar agajin gaggawa na kasar ciki har da sojoji da 'yan sanda, har yanzu na ci gaba da neman mutanen da ba a gano ba.

    To amma fatan iyalan wadanda ba a kai ga gano su ba yanzu na cewa suna raye ya ragu.

    An bayyana ambaliyar ruwan a matsayin mummunan masifar da aka shafe gomman shekaru ba a ga irinta ba a Afirka ta Kudu.

    Har yanzu ba a kai ga kiyasta irin dumbin asarar da aka tabka ba sakamakon ambaliyar, to amma kididdigar da aka yi ta farko ta nuna cewa an yi asarar fiye da dala biliyan daya da miliyan dari biyar.

    Dukkan wasu manyan ababan more rayuwa a yankin da gidajen mutane da hanyoyin ruwa da turakun wutar lantarki duk sun lalace.

  12. Cutar korona ta kashe sama da mutum miliyan daya a Amurka

    Fadar gwamnatin Amurka ta ce adadin wadanda suka mutu saboda cutar korona ya zarta miliyan guda.

    Shugaban kasar Joe Biden, ya ce kasar ta yi asara mai yawa na mutanen da ba za a manta da su ba.

    Adadin na Amurka shi ne mafi yawa a duniya,kodayake hukumar lafiya ta duniya ta ce za a iya samun adadin wadnad asuka mutu da ya zarta na Amurkan a wata kasa.

    Kazalika ya zuwa yanzu an samu adadin wadanda suka kamu da cutar koronar a kasar fiye da miliyan 80 a cikin al'ummar kasar da yawansu ya kai miliyan 330.

    A ranar 20 ga watan Janairun 2020, ne aka samu mutum na farko daya kamu cutar korona bayan ya dawo daga Wuhan na kasar China.

    Kwararru a bangaren lafiya a kasar sun bayyana dalilan da ya sa aka samu wadanda suka mutu da dama a Amurka, inda suka akwai yawan masu teba da hawan jini da kuma yawan tsofaffi da kasar ke da su.

  13. Masu kashe zabiya za su sha ɗaurin shekara 155 a gidan yari a Malawi

    Wata babbar kotu a Malawi ta yanke wa wasu mutum uku hukuncin zaman gidan kaso na tsawon shekara 155 kowannensu saboda kashe zabiya.

    Mutanen masu shekara 44 da 45 da kuma 71, an same su da laifi bayan sun amsa cewa su suka kashe wani zabiya dan shekara 23 a farkon shekarar 2022.

    Daya daga cikin mutane da aka yankewa hukuncin kawun zabiyan da aka kashe ne.

    Fiye da shekara 10, Malawi na fuskantar hare-hare da kuma kisan a kan zabiya, wanda ake dangantawa da camfe-camfe da kuma amfani da wasu sassan jikinsu don yin arziki.

    Tun daga shekarar 2014,an samu tuhume-tuhume 170 a kan kisa ko cin zarafin zabiya a kasar.

  14. Buhari ya bai wa gwamnan CBN umarnin sauka daga mukaminsa idan yana son takara

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bai wa gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele, da wasu masu rike da mukaman siyasa da ke neman tsayawa takara umarnin su sauka daga mukamansu.

    Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha ya fitar bisa umarnin shugaban kasar.

    Shugaban Najeriyar ya lura da cewa akwai wasu manyan jami'ai a gwamnatinsa da ke son tsayawa takarar mukaman siyasa daban-daban, shi ya sa ya bayar da wannan umarnin.

    Emefiele na fuskantar matsin lamba tun bayan da wasu kungiyoyi suka saya masa fam din tsayawa takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar APC.

  15. Majalisar wakilan Najeriya ta roki China ta taimaka wajen kubutar da fasinjojin jirgin kasar da aka sace

    Kwamitin kula da harkokin sufuri a majalisar wakilan Najeriya, ya roki gwamnatin China da ta taimaka wajen ganin an kubutar da fasinjojin jirgin kasan nan 62 da aka sace a ranar 28 ga watan Maris a kan hanyarsu ta zuwa Kaduna daga Abuja.

    Shugaban kwamitin Sanata Abdulfatai Buhari, wanda ya yi magana a madadin 'yan kwamitin a yayin wata ziyarar gani da ido da kwamitin ya kai tashar jirgin kasa ta Obafemi Awolowo da ke Ibadan ya bayyana rashin jin dadinsa a kan rashin kubutar da mutanen har kawo yanzu.

    Sanatan ya ce harin da aka kai kan jirgin kasan ya sanya fargaba a zukatan 'yan Najeriya wadanda suka koma tafiye-tafiye ta jirgin.

    Ya ce, ba laifi ba ne idan gwamnatin China ta zo ta taimaka wa Najeriya wajen ceto fasinjojin.

    Kamfanin kasar China ne dai ya gina layin dogon da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna wanda ke da nisan kilomita 159.

    Sanatan ya ce, gwamnatin China ta samu kudi daga irin ayyukan da kamfaninta na CCECC ya yi a Najeriya, don haka ba gazawa ba ce idan an nemi su zo su taimaka.

  16. Google zai kara yaruka 24 cikin fassararsa

    Katafaren kamfanin harkokin fasaha na duniya Google, ya sanar da ƙara sabbin harsuna guda 24 a rumbunsa na fassara.

    Matakin ya kawo jimillar harsunan da Google ke fassarawa zuwa 133.

    Goma daga sabbin harsunan da Google din ya ƙara yaruka ne na al'ummar Afirka.

    Yarukan Afirka da Google din ya kara sun hada da Lingala da Twi da kuma Tigrinya.

    Google ya ce ya dauki matakin ne domin taimaka wa wadanda yarukansu ba sa kan yawancin shafukan fasaha.

    Sauran yarukan da ya kara sun fito ne daga al'ummar Bhojpuri wanda mutum miliyan 50 a arewacin India ke amfani da shi, da Nepal da kuma Fiji wadanda su ma akwai masu amfani da su da dama.

    A shekarar 2020 ne Google ya ƙara yaruka biyar.

  17. 'Yan Ghana na ji a jikinsu kan hauhawar farashin kayayyaki a kasar

    Hauhawar farashin kayayyaki a Ghana ta kai kashi 23 da digo 6 cikin 100, ƙari mafi sauri da aka samu tun daga watan Maris din da ya wuce.

    Wani mai kididdiga a gwamnatin kasar, Kobina Annim, ya bayyana cewa farashin kayayyakin da ake shigowa da su ya fi ƙaruwa a kan wadanda ake yi a gida.

    Tuni dai 'yan kasar ta Ghana suka fara alawadai a kan karuwar farashin kayan abinci da sauran kayayyakin bukatun yau da kullum abin da suka ce sun shiga cikin tsaka mai wuya.

    Ana ganin hahhawar farshin kayayyakin da za ta iya shafar bunkasar tattalin arzikin kasar.

    Kazalika kasar waddda ita ce ta biyu da ke da karfin tattalin arziki a kasashen yammacin Afirka, na fama da karin farashin harkokin da suka shafi sufuri da ruwa da iskar gas da ma wutar lantarki.

    Tuni kungiyoyin ƙwadago suka yi kira ga gwamnatin kasar da ta rinka warewa ma'aikatan gwamnati alawus na daban bisa la;akari da yadda al'amura ke tafiya a kasar.

  18. Koriya ta Arewa ta ce cutar korona ta ɓulla a ƙasar a karon farko

    A karon farko, Koriya ta Arewa ta amince da barkewarta cutar korona a hukumance.

    Kafofin yada labaran kasar sun ce Shugaba Kim Jong-un ya jagoranci wani taro don tattauna abin da ya bayyana a matsayin "babban abu da ke bukatar a ba shi kulawar gaggawa.

    Barkewar wadda aka fara ganowa a babban birnin kasar Pyongyang ranar Lahadi, ta hada da nau'in Omicron mai saurin yaduwa.

    Wakiliyar BBC ta ce mai yiwuwa ne an samu wadanda suka kamu a baya, da mahukunta suka yi tunanin za su shawo kan lamarin cikin hanzari.

    Ba a bayar da cikakken bayani kan adadin wadanda suka kamu da cutar ba.

    Koriya ta Arewa ta rufe iyakokinta a farkon barkewar cutar kuma ta yi ikirarin hana ta shiga kasar a wancan lokaci.

  19. Antonio Guterres ya yi kira da a gudanar da bincike kan kisan 'yar jaridar Al Jazeera

    Sakatare-janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya ce ya kadu matuka da kisan gillar da aka yi wa fitacciyar 'yar jaridar Al Jazeera, Shireen Abu Akleh.

    An harbe ta ne a jiya Laraba, a lokacin da take ba da labarin farmakin da sojojin Isra'ila suka kai a gabar yammacin kogin Jordan da suka mamaye.

    Mista Guterres, ya shiga sahun masu kiran a gudanar da bincike mai zaman kansa kan mutuwarta.

    Isra'ila ta ce mai yiwuwa 'yan bindigar Falasdinawa ne suka harbe Abu Akleh.

    Sai dai wani dan jarida da ya samu rauni a lokacin kisan na ta, Ali Samoudi, ya shaida wa BBC cewa babu wasu Falasdinawa 'yan bindiga a kusa da inda abun ya faru.

  20. Jirgin sama ya yi hadari da mutum 11 a Kamaru

    Ma'aikatar kula da harkokin sufuri a Kamaru ta ce wani karamin jirgin saman fasinja da ke ɗauke da mutum 11 ya yi hadari a wani daji da ke kudu da Yaounde babban birnin Kamaru a jiya Laraba.

    Har yanzu ba a san musababbanin abin da ya haddasa hadarin ba, to amma rahotannin sun ce sadarwa ta katse tsakanin filin jirgin da kuma matuƙan jirgin.

    Daga bisani an gano shi a kusa da wani daji da ke kusa da Nanga Eboko da ke da nisan kilomita 150 daga Yaounde.

    Jirgin ya tashi ne daga filin jirgin saman Nsimalen zuwa Belabo da ke gabashin kasar in ji ma'aikatar sufurin.

    Kamfanin dillancin labarai na AFP, ya ruwaito cewa wani kafanin Mai mai zaman kansa mai suna COTCO ne ya yi shatar jirgin.

    Wannan ne dai karo na farko da aka samu babban hadarin jirgin sama a kasar tun shekarar 2007, a lokacin da jirgin saman Kenya dauke d afasinjoji 114 ya yi hadari jim kadan bayan ya tashi da ga Douala.