An kama jami'an tsaron Najeriya dauke da kudin fansa Naira miliyan 60

Wasu jami'an tsaro da ke dauke da Naira miliyan 60 sun shiga hannun hukumomi.
Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa an kama jami'an tsaron ne bayan da wasu suka fallasa cewa suna dauke da kudin fansa kuma suna kan hanyar kai kudin ne ga barayi daji.
Sojojin kasa na Najeriya tare da taimakon wasu dakarun sojin sama ne suka kai wani samame a yankin wada ya sa aka halaka wasu 'yan fashin daji da kuma ceto wadanda aka yi garkuwa da su.
Wani jami'in tsaro na cikin gida ya shaida wa jaridar PRNigeria cewa "An kwace tsabar Naira miliyan 60 tare da man fetur da wasu bindigogi samfurin AK-47 da wayoyin hannu da kuma harsasai masu yawa."











