'Yan bindiga sun kashe 'yan sandan Najeriya uku a Enugu
An shiga rudani da fargaba a cikin garin Enugu bayan da wasu ‘yan bindiga suka kasha ‘yan-sanda uku a wani wurin binciken ababan hawa, Alhamis din nan da rana.
Lamarin ya faru ne kamar yadda rahotanni suka ce da kusan karfe 1:20 na rana, a kusa da rukunin gidaje na
Ulumalinda a wajen karamar hukumar Enugu ta kudu.
An ce ‘yan bindigar sun sace wata mata a yayin farmakin, wanda aka ce sun kai minti talatin suna cin karensu ba babbaka.
Haka kuma sun ‘yan bindigar sun yi wa wata mata mai sana’ar karba da bayar da kudi (POS) fashi bayan da harsashi ya same ta.
Kakakin ‘yan-sanda na jihar, Daniel Ndukwe, ya tabbatar wa da maneman labarai lamari, amma bai yi Karin bayani ba.