Korona ta kashe ƙarin mutum shida a Najeriya
Hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce cutar korona ta kashe ƙarin mutum shida ranar Lahadi a ƙasar.
Haka nan, hukumar ta ce an samu ƙarin mutum 537 da suka kamu da cutar.
Sabbin kamuwar sun fito ne daga jiha takwas, ciki har da Abuja babban birnin Najeriyar. Jihohin su ne:
- Rivers (313)
- Lagos (178)
- Abuja (19)
- Kaduna (11)
- Gombe (6)
- Ogun (6)
- Ekiti (3)
- Abia (1)
Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 248,312 ne aka tabbatar sun harbu da cutar a Najeriya, yayin da 3,077 suka rasa rayukansu.