Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Gwamnatin Kaduna za ta kori malaman makaranta 233

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist (@kaitamustapha)

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Alhamis idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Za ku iya ziyartar shafinmu na Facebook ko Twitter ko kuma na Instagram domin bayyana ra'ayoyinku kan irin labaran da muke wallafawa ko kuma tafka muhawara a kai.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin:

    • Erdogan ya kori ministansa na kuɗi saboda faɗuwar darajar kuɗin Turkiyya
    • Dalilan da suka hana buɗe layukan waya a Zamfara
    • Wasu sun ƙone wani ɓangare na ofishin Sanata Barau Jibrin a Kano
    • Majalisar Ɗinkin Duniya na son a tara mata dala biliyan 41
    • Nau’in korona na Omicron ya zama alaƙaƙai a Afrika ta Kudu
    • Kotu ta buƙaci a ba shugaban IPOB Nnamdi Kanu ‘cikakkiyar walwala’
    • Hazo ya sa an rufe makarantu a Indiya
    • Gwamnatin Kaduna za ta kori malaman makaranta 233

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai.

  2. Yadda aka kai hari ofishin APC na Sanata Barau Jibrin a Kano

  3. Jamus na barazanar mayar da riga-kafin korona tilas shekara mai zuwa

    Gwamnatin Jamus ta sanar da cewa akwai yiwuwar a shekara mai zuwa za a mayar da riga-kafin korona tilas.

    Shugabar gwamnatin Jamus, Angela Merkel ta bayyana cewa tana goyon bayan wannan matakin wanda ƴan majalisar ƙasar ke son yin ƙuri'a a kai a watan Fabrairu.

    Mrs Merkel ta kuma bayyana cewa akwai wasu takunkumai da za a saka wa waɗanda ba su yi riga-kafin ba.

    Ta ce ba za a bari su shiga gidajen sayar da abinci ba da wuraren kallo da wuraren shaƙatawa ba.

    Sai dai dokar ba za ta shafi waɗanda ba su daɗe da farfaɗowa daga cutar ba.

    A halin yanzu dai Jamus na fuskanatar ɓullar cutar karo na biyu inda alƙaluman baya-bayan nan ke nuna cewa akwai mutum 400 da cutar ta kashe.

  4. Masu iƙirarin jihadi sun kashe sojoji biyu a Benin

    Sojoji a Benin sun bayyana cewa mayaƙa masu iƙirarin jihadi sun kashe sojoji biyu da kuma raunata da dama a lokacin da aka kai hari a arewacin ƙasar.

    Ba a cika kai hare-hare a Benin ba sai dai mayaƙa da ke da alaƙa da al Qaeda da kuma IS na kai hare-hare a makwaftanta daga arewaci kamar Burkina Faso da Nijar.

    A daidai lokacin da rashin tsaro ke ƙara ƙaruwa a yankin Sahel, akwai damuwa ƙwarai kan cewa ƙasashe kamar su Benin da Ivory Coast da Ghana da Togo za su fuskanci wannan barazana.

  5. An kama 'ƴan daba' 13 a Kano waɗanda ake zargi da kai hari ofishin Sanata Barau

    Ƴan sanda a jihar Kano sun kama mutum 13 da ake zargin ƴan daba ne waɗanda ke da hannu a ƙona wani bangaren ofishin Jam'iyyar APC na Sanata Barau Jibrin.

    Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar yan sandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana haka a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

    Ya bayyana cewa cikin abubuwan da aka kama matasan da su har da muggan makamai 34, da gorori 23 da galan biyu na abin da ake zargi fetur ne da layoyi da dai sauransu.

    Da safiyar yau ne wasu matasa suka ƙone wani ɓangare na ofishin sanata Barau Jibrin a Kano, jigo a ɓangaren APC da ya raba gari da ɓangaren gwamnan jihar.

    Shaidu sun bayyana wa BBC cewar matasan sun fi 100 da suka afka wa ofishin jam’iyyar.

  6. Kotu a Libya ta wanke Saif al-Islam ɗan gidan Gaddafi domin tsayawa takara

    Wata kotu a Libya ta wanke dan gidan tsohon shugaban Libya Muammar Gaddafi domin yin takara a zaben shugaban kasar, da za a gudanar a wannan wata na Disamba da kuma Janairu na shekara mai zuwa.

    Kafin hukuncin kotun na yau, hukumar zaben kasar ta dakatar da Saif al-Islam Gaddafi daga yin takarar shugaban kasa, saboda hukuncin wata kotu a shekara ta 2015, wadda ta yanke masa hukuncin kisa saboda aikata laifukan yaki, lokacin da baya kasar.

    A yau ne lauyoyinsa suka samu damar daukaka karar a gaban wata kotu da ke birnin Sabha, bayan da ƴan bindiga suka hanasu gabatar da ƙarar a cikin makon da ya gabata.

    Wannan na zuwa ne bayan hukuncin wata kotu dake birnin Zawiya, wadda ta tabbatar da soke takarar jagoran dakarun yan awaren gabashin kasar Khalifa Haftar a wannan makon. Za a gudanar da zaben shugaban kasar zagaye na farko ne a ranar 24 ga wannan wata na Disamba.

  7. Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmad Sulaiman kwamishina

    Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmed Sulaiman kwamishina na biyu a hukumar kula da makarantun firamare ta jihar Kano.

    Alaramma Ahmad Sulaiman ne ya tabbatar da ba shi wannan muƙamin a saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook inda ya yi godiya ga gwamnan.

    Ya wallafa hotunansa tare da gwamnan, a gefe akwai Sheikh Abdullahi Balalau wanda shi ne shugaban Ƙungiyar Izala, da kuma sakataren ƙungiyar na ƙasa Sheikh Kabir Gombe.

    Malam Ahmad Sulaiman ya roƙi Allah ya sa albarka a kujerar da ya samu da kuma roƙon addu'ar jama'a kan taya sa riƙo.

  8. Sergi Roberto: Barcelona za ta yi wa dan wasanta tiyata

    Barcelona ta sanar da cewar likitoci za su yi wa Sergi Roberto tiyata a raunin da yake damunsa a kafarsa ta hagu.

    Dakta Lasse Lempainen zai yi aikin a Turku a Finland tare da kulawar likitocin Barcelona, haka kuma kungiyar ta ce za ta sanar da sauran bayanai kan lokacin da zai yi jinya, idan an yi masa aikin cikin nasara.

    Duk da raunin da yake damun Roberto ya buga wa Barcelona wasa 12 a kakar nan, inda tara daga ciki a La Liga da kuma fafatawa uku a Champions League.

    Ga cikakken labarin a nan:

  9. Nau’in Omicron na korona ya shiga Ghana

    Ghana ta tabbatar da samun sabon nau'in korona na Omicron a kasar amma jami'an sun ki bayyana adadin mutanen da suka kamu da cutar.

    Hukumomi sun ce an samu cutar ne a jikin wasu matafiya wadanda suka isa kasar ta filin jirgin saman Kotokana kasa da kasa da ke Accra.

    An soma samun sabon nau'in cutar na Omicron ne a Afirka ta Kudu kuma kawo yanzu kasashe fiye da 20 ne suka bayar da rahoton bullar nau'in.

  10. Hamid Karzai ya roki Amurka ta tallafawa gwamnatin Taliban

    Tsohon shugaban kasar Afghanistan Hamid Karzai ya shawarci Amurka ta taimaka wajen sake gina kasar.

    Cikin wata tattaunawa da yayi da BBC, Mr Karzai ya bayyana cewa, dole Amurka tayi aiki da Taliban kasancewar suke da rike da madafun ikon kasar.

    Tsohon shugaban ya kuma kara da cewa akwai bukatar Amurka da kawayenta su magance illar da sukayiwa kasar cikin shekaru ashirin da suka gabata.

    Mr Karzai, wadda Amurka ta kaddamar da yaki kan kasar yayin gwamnatinsa ya bayyana cewa baya son cigaba da ganin kasar na dogaro kan tallafi daga wajen kasar.

  11. Gwamnatin Kaduna za ta kori malaman makaranta 233

    Hukumar ilimin bai-ɗaya ta jihar Kaduna za ta kori malamai 233 da ake zargi sun gabatar da takardun makaranta na bogi.

    A cikin jawabin shugaban hukumar Tijjani Abdullahi da gwamnan Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya wallafa a Facebook ya ce an tantance takardun malamai 451 ta hanyar tuntuɓar makarantun da malaman suka yi iƙirarin sun yi.

    Shugaban ya ce bahasin da makarantu 13 suka bayar ya nuna malamai 233 takardun jabu suka gabatar.

    Ya ce ɗaya daga cikin makarantar da aka tura wa takardun malaman ta nesanta kanta da shedar karatu 212 daga cikin 233.

    “Don haka hukumar za ta kori malamai 233 da suka gabatar da takardun makaranta na jabu kuma za a gabatar da takardunsu ga ma’aikatar shari’a domin fuskantar hukunci. “

    Hukumar ta ce za ta ci gaba da tantance sahihanci takardun malaman jihar a matsayin ɗaya daga cikin matakan da gwamnatin Kaduna ke ɗauka da farfaɗo da ilimi.

    Hukumar ta kuma ce za ta yi wa malaman jihar 12,254 jarabawar gwaji da horo wanda za a fara daga watan Janairun 2022

  12. Hazo ya sa an rufe makarantu a Indiya

    Hazo ya sa an rufe makarantu a Delhi daga ranar Juma’a, kuma ministan muhalli Gopal Rai ya ce zuwa yanzu babu ranar buɗe makarantun.

    Rufe makarantun na zuwa bayan hukuncin kotun ƙoli da ta ƙalubalanci hukumomin babban birnin ƙasar kan buɗe makarantun duk da ƙazancewar gurɓatacciyar iskar a Delhi.

    Kotun ta nemi sanin dalilin da ya sa yara za su koma makaranta yayin da manya ke aiki daga gida.

    A watan da ya gabata kotun ƙoli ta ba da umarni ga gwamnatin Delhi da gwamnatin Indiya da su gaggauta ɗaukar mataki na magance matsalar a Delhi.

  13. Kotu ta buƙaci a ba shugaban IPOB Nnamdi Kanu ‘cikakkiyar walwala’

    Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), da ta tabbatarda shugaban ƙungiyar ƴan a-waren Biafra Nnamdi Kanu ya samu ‘cikakkiyar walwala’ yayin da yake tsare a hannunsu.

    Umurnin ya biyo bayan ƙorafin da lauyoyinsa suka yi na cewa wanda suke karewa an hana shi walwala ko canza kayada yin addininsa ba ya iya wa a yayin da yake tsare.

    Sauraren shari’ar gaggawar da aka yi ya biyo bayan ƙorafin da lauyoyinsa suka yi cewa ɗage shari’ar da aka yi tun da farko ya saɓawa sauraren shari’ar cikin hanzari da aka shirya yi wa shugaban na IPOB.

    Kanu wanda ake tuhuma da cin amanar ƙasa bai halarci zaman kotun ba a ranar Alhamis. An ɗage shari’ar zuwa ranar 18 ga watan Janairun 2022.

    A kwanakin baya shugabannin ƙabilar Igbo suka roƙi shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya saki Nanmdi Kanu, buƙatar da shugaban ya ce ta yi nauyi sai ya yi nazari.

  14. Nau’in korona na Omicron ya zama alaƙaƙai a Afrika ta Kudu

    Jami’an lafiya a Afrika ta Kudu sun ce sabon nau’in korona na Omicron ya zama ruwan dare a Afrika ta Kudu yayin da ake ci gaba da samun waɗanda suka kamu a ƙasar.

    Alƙalumman baya bayan nan sun nuna an samu ƙarin mutum 8,500 da suka kamu.

    Adadin ya lunka 4,300 da aka samu a ranar Laraba.

    Yanzu an samu ɓullar cutar a ƙasashe 24 na duniya, a cewar hukumar lafiya ta duniya.

    Afrika ta Kudu ce ta farko da aka fara samun ɓullar sabon nau’in na korona.

    Indiya da Saudiyya da Daular Larabawa na daga cikin ƙasashen da suka sanar da ɓullar cutar. Sauran sun haɗa da Birtaniya da Amurka da Jamus.

    Mutum uku cutar ta kama a Najeriya.

  15. ‘Yawan sumbata a bukukuwan kirsimeti na iya yaɗa korona’

    Gwamnatin Birtaniya ta yi gartgaɗi ga ƴan ƙasar kada su dinga sumbatar duk wanda ba su sani ba a lokacin bukukuwan Kirsimeti don rage yaɗuwar annobar korona.

    Sakatariyar ayyuka da fansho Therese Coffey ta ce ya kamata mutane su ji daɗin Kirsimeti amma: "Ba na jin ya kamata a dinga sumbata da yawa".

    Ɗan jaridar kafar ITV Robert Peston ya tambaye ta ko ya kamata jama'a su takaita cuɗanya tsakaninsu a makwanni masu zuwa.

    Ta ce gwamnatin Birtaniya na ƙoƙarin tabbatar da jin daɗin al’umma.

    A ƴan kwanakin nan ana fuskantar barazanar ɓullar sabon nau’in korona na Omicron inda wasu ke ganin zai kawo cikas ga bukukuwa kirsimeti.

  16. Majalisar Ɗinkin Duniya na son a tara mata dala biliyan 41

    Majalisar dinkin duniya ta yi kira ga kasashen duniya da su hada mata dala biliyan 41, domin ta gudanar da ayyukan jin-kai a badi.

    Ba a taɓa neman yawan wannan kuɗin ba domin tafiyar da ayyukan jin-kai na majalisar Ɗinkin Duniya.

    Majalisar ta ce mabuƙata agajin gaggawa za su karu da kashi 17 a 2022.

    Majalisar ta yi ƙiyasin cewa mutum miliyan 274 ne za su buƙaci tallafin gaggawa a shekarar ta 2022.

    Rikici a ƙasashen Yemen da Syria da Habasha, da kuma matsalar sauyin yanayi na daga abubuwan da suka ta'azzara lamarin.

  17. Buhari ya isa Dubai

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya isa birnin Dubai domin halartar taron kasuwanci na EXPO 2020 da ake yi duk shekara shekara.

    Fadar shugaban ta wallafa hotunan shugaban lokacin da hukumomin Daular Larabawa ke tarbarsa.

  18. Wasu sun ƙone wani ɓangare na ofishin Sanata Barau Jibrin a Kano

    Wasu matasa sun ƙone wani ɓangare na ofishin sanata Barau Jibrin a Kano, jigo a ɓangaren APC da ya raba gari da ɓangaren gwamnan jihar.

    Shaidu sun bayyanawa BBC cewar matasan sun fi 100 da suka abka wa ofishin jam’iyyar.

    Wannan na zuwa a yayin da wata kotu a Abuja ta rushe shugabancin ɓangaren gwamna Ganduje tare da tabbatar da jagorancin ɓangaren Shekarau.

    Rikicin siyasar APC a Kano na ci gaba da ɗaukar hankali a Najeriya tun bayan gudanar da zaɓen shugabannin jam’iyyar ɓangare biyu, inda wasu ke ganin rabuwar kai a Kano wata babbar ɓaraka ce ga APC.

  19. Dalilan da suka hana buɗe layukan waya a Zamfara

    Gwamnatin Zamfara ta bayyana wasu dalilai da ta ce ya sa har yanzu ba dawo da layukan sadarwa ba a yankunan jihar.

    Sanarwar da kwamishinan watsa labaran jihar Ibrahim Dosara ya fitar ta ce umarnin da gwamnan jihar ya bayar na dawo da layukan sadarwar yana nan amma sanarwar ta faɗi hanyoyin da ta ce ake bi domin dawo da hanyoyin sadarwar.

    A cewar gwamnatin Zamfara, matakan sun haɗa da tsarin doka da sa hannu kan umarnin wanda zai ba da izinin sa ke dawo da layukan sadarwar.

    Da nazari kan yanayin tsaro a ƙananan hukumomi 14 na jihar don tabbatar da irin shirye-shiryen da za a yi bayan dawo da hanyoyin sadarwar.

    “Dole sai buƙatar daga ministan sadarwa da hukumar NCC ta dace da rahoton tsaro da sauran matakan da suka dace,” in ji sanarwar.

    Gwamnatin Zamfara ta ce gwamnan jihar na dab da sa hannu kan umarnin.

  20. Erdogan ya kori ministansa na kuɗi saboda faɗuwar darajar kuɗin Turkiyya

    Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdowan ya sauke ministansa na kudi, yayin da darajar kuɗin ƙasar ta lira ke taɓarɓarewa.

    Shekara ɗaya kawai Lufti Elvan ya yi akan muƙaminsa na ministan kuɗi, kuma kamar yadda rahotanni suka nuna sun samu saɓani da mai gidansa kan tsarin da za a bi wurin farfaɗo da darajar ta Lira.

    Yanzu haka darajar Lira ta fadi da kashi 40a kan dalar Amurka, kuma ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayayyaki a Turkiya.