Korona ta kama ƙarin mutum 21 a Najeriya
Hukumar ɗakile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce an samu ƙarin mutum 21 da suka kamu da cutar korona a Najeriya.
Alƙalumman sun nuna mutum shida suka kamu da cutar a Legas, jihar da cutar ta fi bazuwa, sai a jihar Cross Rivers da aka samu mutum biyar a ranar Litinin.
A jihar Rivers an samu mutum biyar, sai jihar Ondo mai mutum uku. A Kaduna ƙarin mutum ɗayaaka samu haka ma a Bauchi.
Yanzu jimillar mutum 214,113 cutar ta shafa a Najeriya amma 207,297 sun warke yayin da cutar ta kashe mutum 2,976 a Najeriya.
Ga jihohin da aka samu ƙarin cutar a Najeriya a ranar Litinin.
Lagos-6
Cross River-5
Rivers-5
Abia-3
Bauchi-1
Kaduna-1