Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Buhari ya ce zai hukunta masu daukar ma'aikatan boge da cushen albashi

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau and Badariyya Tijjani Kalarawi

  1. Korona ta kama ƙarin mutum 21 a Najeriya

    Hukumar ɗakile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce an samu ƙarin mutum 21 da suka kamu da cutar korona a Najeriya.

    Alƙalumman sun nuna mutum shida suka kamu da cutar a Legas, jihar da cutar ta fi bazuwa, sai a jihar Cross Rivers da aka samu mutum biyar a ranar Litinin.

    A jihar Rivers an samu mutum biyar, sai jihar Ondo mai mutum uku. A Kaduna ƙarin mutum ɗayaaka samu haka ma a Bauchi.

    Yanzu jimillar mutum 214,113 cutar ta shafa a Najeriya amma 207,297 sun warke yayin da cutar ta kashe mutum 2,976 a Najeriya.

    Ga jihohin da aka samu ƙarin cutar a Najeriya a ranar Litinin.

    Lagos-6

    Cross River-5

    Rivers-5

    Abia-3

    Bauchi-1

    Kaduna-1

  2. Maraba

    Muna maku maraba da kasancewa da mu a wannan shafin da za mu kawo maku labarai da rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.