Sojojin Najeriya 'sun fatattaki' 'yan Boko Haram daga Damboa
Mazauna garin Damboa na Jihar Borno sun wayi gari cikin murna sakamakon nasarar da sojoji suka yi ta daƙile harin mayaƙa masu iƙirarin jihadi a safiyar yau Juma'a, a cewar rahoton Daily Trust.
Jaridar ta ruwaito cewa maharan sun afka wa garin da misalin ƙarfe 6:35, inda suka dinga harbi kan mai tsautsayi.
Fafatawar ta sanya mayaƙan suka fice daga garin bayan minti 30, kamar yadda wata majiyar tsaro ta shaida wa jaridar.
"Ina tabbatar muku Boko Haram sun kawo hari da safiyar nan amma ba su yi nasara ba a Damboa saboda sojoji sun fatattake su nan take," in ji majiyar.
A ranar Asabar da ta gabata rundunar sojan Najeriya ta ce ta kashe gwamman mayaƙan ISWAP da suka kai wa sansaninta hari a Askira, sai dai lamarin ya yi sanadiyyar kashe Birgediya Janar Dzarma Zurkushu.
Wani ɗan banga ya bayyana cewa mayaƙan sa-kai 10 sun ji raunukan harbin bindiga a Kala da ke kusa da Damboa.