Buhari ya isa birnin Glasgow lafiya
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya isa birnin Glasgow na Scotland lafiya domin taron sauyin yanayi.
Shugaban zai hadu da shugabanni sama da 120 da za su halarci taron
Wata sanarwa da kakakin shugaban kasar, Garba Shehu ya aike wa manema, ta ce sai a ranar Talata Buhari zai gabatar da nasa jawabin a wurin taron sannan kuma zai bayyana irin matakan da ƙasarsa ke ɗauka wajen rage ɗumamar yanayi.
Ana sa ran shugaban zai gana da shugaban Amurka Joe Biden da kuma na Faransa Emmanuel Macron.
Taron sauyin yanayin da aka yi wa lakabi da COP 26, taro ne da Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya domin duba inda aka kwana bayan taron Paris da aka gudanar a shekarar 2015.