Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Ba abu ba ne mai sauki rike ma'aikatar noma - Nanono

Labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Imam Saleh, Nasidi Adamu Yahaya and Buhari Muhammad Fagge

  1. An ga hayaƙi a tashar sararin samaniyar duniya

    An kaɗa ƙararrawar gargaɗi a tashar sararin samaniyar duniya, bayan da ma’aikatan jirgin suka bayar da rahoton ganin hayaki mai wani irin ƙauri kamar ana ƙona roba.

    Lamarin ya fi kamari a wani yanki da ake kira Zvezda da Rasha ta gina a matsayin wurin yada zango ga halittu'' in ji rahoton kafofin watsa labaran Rasha.

    Tashar sararin samaniyar da ta shafe shekaru aru-aru ta sha fama matsaloli a shekarun baya bayan nan, don ko a kwana-kwanan nan sai da wani jami’in Rasha ya yi gargadin cewa wasu naurori sun lalace.

    Hukumar kula da sararin samaniyar Rasha ta ce bayan samun matsalar, injina sun ci gaba da aikinsu ba tare da wata matsala ba.

    An gano hayakin ne yayin cajin batirin tashar, in ji hukumar, kuma yanzu ma’aikatan jirgin sun koma “horo na yau da kullum”.

    An ce ƙaurin kona robar da ake ji a yanzu ya fara kai wa ga bangaren da Amurka ta samar a tashar sararin samaniyar.

    Hukumar kula da sararin samaniya ta Amurka, Nasa, ta ce hakan ba zai hana ta aika ƴan sama jannatin da ta tsara yi ranar Alhamis ba.

    Ku karanta cikakken bayani a kan Cibiyar Kimiyya Ta Sararin Samaniya.

  2. Ƴan bindiga sun sace ma'aikatan tsohon shugaban Najeriya

    Ƴan bindiga sun sace wasu ma'aika a gonar tsohon shugaban Najeriya Oluseagun Obasanjo a garin Kobape da ke jihar Ogun.

    Rahotanni sun ce maharan sun faki mutanen ne, tare da budewa motarsu wuta, kana daga baya suka yi awon gaba da su.

    Ko da yake ba a bayyana sunayen mutanen ba, amma manyan jami'ar katafariyar gonar tsohon shugaban ƙasar ne.

  3. Ana zargin shugaban Brazil da goyon bayan masu aikata laifi

    Babban alƙalin kotun ƙolin Brazil, ya zargi shugaban ƙasar Jaire Bolsonaro da kai hari ga dimokraɗiyya ta hanyar ba waɗanda suka saɓa wa hukuncin kotu goyon baya.

    Alƙalin kenan yake cewa da ƙarfin dimokraɗiyya da na hukumomi, kotun koli ba za ta taɓa lamuntar barazana ga ƴancin kanta ba ko kuma neman kawo mata wargi idan tana kokarin gudanar da ayyukanta.

    Kalaman na alƙalin na zuwa ne, kwana guda bayan da ya shaida wa magoya bayansa cewa ba zai bi umarnin ɗaya daga cikin alƙalan ba, da ke yi wa shugaban shari'a kan zargin yaɗa labaran ƙarya.

  4. Ana zargin Facebook da yi wa dokokin Birtaniya hawan ƙawara

    Ana zargin kamfanin Facebook da saɓa dokar daidaito a Birtaniya yayin da kamfanin ke tallata ayyuka.

    Ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Global Witness ta ce bincikenta ya gano cewa kamfanin Facebook na tallata ayyukan da suka shafi makanikai akasari ga maza, sai kuma kusan duk wata talla ta neman malaman jinya ana yi wa mata ne.

    Wakilin BBC ya ce Ƙungiyar ta yi kira ga kungiyoyi da kuma hukumar kare hakkin bil adama da su gudanar da bincike kan wannan lamari, sai dai Facebook ya ce yana duba wannan ƙorafin kuma shafin na nuna wa mutane tallar abubuwan da suke so ne.

  5. Buɗéwa

      • Marubuci, Imam Saleh
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multimedia Broadcast Journalist

    Jama'a Assalamu alaikum, barkanmu da sake saduwa da ku a wannan shafi da muke kawo muku labaran duniya kai tsaye daga nan sashen Hausa na BBC.

    Nine Imam Saleh, nake muku maraba, da fatan za ku kasance tare da mu a wannan rana don jin irin abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya baki daya.