Taliban: Ina 'yan gudun hijira za su tafi bayan Taliban ta karbe iko?
A yanzu dai babu takamaiman adadin 'yan gudun hijirar da ke barin ƙasar, amma zuwa yanzu an kwashe mutum fiye da 30,000 daga ƙasar.
Ƙungiyar Taliban ta karbe iko da duka iyakokin Afghanistan da maƙotan ƙasashe, kuma mayakan sun ce ba sa son 'yan kasar su fice.
Rahotanni na cewa 'yan kasuwa ne kawai da wadanda ke da shaidar tafiya ake bari su tsallaka.
"Mafi yawan 'yan Afghanistan ba a bari su bar ƙasar ta hanyoyin da aka saɓa," kamar yadda kakakin shugaban hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ya bayyana ranar Juma'a. "Ya zuwa yanzu mutanen da suka fi zama cikin haɗari ba su da hanyar barin kasar nan."
Amma wasu da yawa na ta kokarin ficewa daga kasar ta hanyoyi daban-daban.
Da dama daga cikin 'yan kasar sun haure zuwa Pakistan jim kadan bayan Taliban ta karɓe iko, yayin da ake bayar da rahoton sama da 1,500 na daban sun tsallaka zuwa Uzbekistan kuma duka suna zaune a tantunan da aka kafa kusa da kan iyaka.
A Kabul, dubban mutane ne suke ta nufar filin jirgi, kuma shi kaɗai ne ke aiki a fadin kasar baki daya a wani yunkuri da ake yi na neman ficewa daga kasar.