Kotun Musulunci ta yankewa ƴar Kannywood hukunci kan yaɗa 'hoton batsa'

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Umaymah Sani Abdulmumin

  1. Bankwana

    Masu bibbiyarmu a wannan shafin da haka zamu diga aya sai kuma gobe Talata idan Allah ya tashe mu da rai da lafiya. Umaymah Sani Abdulmumin ke cewa a kwana lafiya.

    Ga wasu daga cikin muhimman labaran da muka kawo muku a yau

    • Ƴan bindiga su kashe mutane da garkuwa da 50 a Zamfara
    • Kotun Musulunci ta yankewa ƴar Kannywood hukunci kan yaɗa 'hoton batsa'
    • An ceto sama da mutum 100 daga hannun mayakan jihadi a Mozambique
    • Kotu ta umarci likitoci su janye yajin aiki a Najeriya
    • Matar tsohon shugaban Najeriya ta rasu
    • Ƴan Ethiopia na zanga-zanga kan zargin cin zarafin da Saudiyya ke yi wa baƙi
    • An samu raguwar yawan mutanen da ake kashewa a Najeriya – Bincike
    • Ƙungiyar Fulani ta miƙa waɗanda ake zargi da fashi ga 'yan sanda
    • Shugabar Tanzaniya na shan suka kan muzanta ƴan wasan ƙwallo ƙafa mata
    • An ɗaure tsohon mininsta shekara 12 kan laifin rashawa a Indonesia
    • 'Yan sandan Najeriya sun kama mutum huɗu da zargin fashi
  2. Ƴan bindiga su kashe mutane da garkuwa da 50 a Zamfara

    z

    Ƴan bindiga sun kashe mutum hudu da garkuwa da 50 a garin Goron Namaye da ke karamar hukumar Maradun a jihar Zamfara, a cewar ƴan sanda.

    Kakakin ƴan sanda, SP Muhammad Shehu da ke tabbatar da harin ga manema labarai a Gusau, ya ce maharan sun zo babu adadi inda suka farwa garin a tsakiyar daren Lahadin.

    Ya kuma kara da cewa tuni aka tura jami'an tsaro na musamman yankin.

    SP Muhammad ya ce kwamishinan ƴan sanda CP Yakubu Elkana ya bada umarnin gaggauta kadamar a binciken ganin yada za a ceto mutanen.

    Sannan an umarci mazauna yankin su kwantar da hankali yayinda jami'an tsaro ke iya bakin kokarinsu wajen inganta tsaro a yankin..

  3. An ceto sama da mutum 100 daga hannun mayakan jihadi a Mozambique

    Kafofin yada labarai a Mozambique sun ruwaito cewa sojoji sun ceto mutum fiye da dari wadanda masu kishin Islama su ka yi garkuwa da su a arewacin kasar.

    Wata rundunar hadin gwuiwa ta sojojin Mozambique da Rwanda ce ta ceto mutanen a wani sansanin mayakan da ke cikin wani kungurmin daji.

    Yawancin wadanda aka ceton mata ne da kananan yara, da kuma wadanda su ka manyanta.

    Sojojin Rwanda dubu daya da aka tura Mozambique na samun nasarori a kan masu tayar da kayar bayan sannu a hankali.

    A kwanan nan su ka taimaka wa 'yan kasar kwato birnin Mocimboa da Praia wanda ke gabar teku - wanda masu tayar da kayar bayan su ka rika amfani da shi a matsayin shalkwatarsu.

  4. Taliban: MDD ta rasa yadda za ta shigar da magunguna Afghanistan

    t

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce daruruwan dubban ton na magunguna da ta ke son kai wa Afghanistan su na jigbe a Dubai saboda yamutsin da filin jirgin saman Kabul ya fada.

    Hukumar na son jiragen da ke kan hanyarsu ta zuwa Afghanistan domin kwashe mutane da su rika biyawa Dubai domin taimakawa su yi jigilar kayan.

    Hulkumar Lafiya ta Duniya da UNICEF na kira ga ƙasashe da a samar da wata hanya ta musamman ta shigar da kayayyakin agaji Afghanistan, kuma rashin iya shigar da magungunan na hana su cimma muradun aikinsu a ƙasar.

    Cikin kayayyakin akwai na ayyukan tiyata, da na magance tsananin rashin abinci mai gina jiki da kuma magungunan da za a raba wa kananan yara masu fama da cutar pneumonia.

  5. Ƴan Ethiopia na zanga-zanga kan zargin cin zarafin da Saudiyya ke yi wa baƙi

    Et

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu zanga-zangar sun yi cuncurundo a wajen ofishin jakadancin Saudiyya da ke Addis Ababa suna alla-wadai da cin zarafin da ake yiwa ƴan kasarsu da ke zaune a Saudiyya.

    Masu boren sun yi kira ga gwamnatin Saudiyya ta daina musgunawa ƴan Ethiopia, da kame marasa dalili, garkame mutane da rashin adalci a shari'a da azabtarwa.

    Dubban baƙi Saudiyya ta tusa keyarsu zuwa gida Ethiopia da sauran ƙasashen gabas ta tsakiya a cikin shekarun baya-bayanan.

  6. Kotun Musulunci ta yanke wa ƴar Kannywood hukunci kan yaɗa 'hoton batsa'

    Sadiya

    Asalin hoton, SADIYAFACEBOOK

    Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta garkame wata ƴar wasan Kannywood da kuma ta yi fice a kafar sada zumunta, Sadiya Haruna kan yaɗa hotunan batsa a shafukanta na sada zumunta.

    Tun a ranar Juma'a aka kama Sadiya Haruna mazauniyar Kabuga da ke Kano.

    Aka kuma ci gaba da rike ta har zuwa wannan Litinin ɗin tare da gabatar da ita a kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a Sharada.

    Sadiya ta amsa laifi guda cikin tuhume-tuhumen da aka gabatar a kanta, wanda ya ci karo da sashi na 355 na kudin panal code na 2000.

    Mai shari'a Ali Jibril Danzaki ya yanke mata hukunci tare da umartar ta koma Islamiyya tayi karatu na tsawon wata shida.

    Sannan ya ce a kullum za ta rinƙa zuwa Islamiyyar da rakiyar jami'in Hisbah da kuma sa idon shugaban makarantar.

  7. Taliban ta ce ba zata amince da ranar ficewar dakarun ketare daga Afghanistan ba

    T

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyar Taliban ta ce ba za ta amince a jinkirta ranar da aka shirya dakarun kasashen waje za su fice daga kasar Afghanistan ba.

    Wani kakakin kungiyar Suhail Shaheen, ya ce ranar 31 ga watan Agusta ce rana ta karshe, kuma tsallaka ta zai zama mai hatsari.

    Ya kuma ce Shugaba Biden ya yi alkawarin kwashe dukkan dakarun kasarsa zuwa wannan ranar, kuma jinkirta ficewar na nufin Amurka ta tsawaita mulkin mallakar da ta ke ma Afghanistan ke nan.

    Ya yi gargadin irin martanin da ka iya biyo baya idan aka saba alkawarin kwashe dukkan sojojin kasashen ketaren.

    A wata hira da wani kakakin Taliban ya yi da BBC, kungiyar ta ce mayakanta sun yi wa filin jirgin saman Kabul kawanya ne domin hana kungiyar IS kai hari a wajen, ba domin su hana mutane barin kasar ba ne.

    Ya kuma ce Taliban ta fi son mutane su yi zamansu a kasar domin sake gina ta domin babu wata barazana kan rayukansu da dukiyoyinsu.

  8. Labarai da dumi-dumi, Kotu ta umarci likitoci su janye yajin aiki a Najeriya

    L

    Asalin hoton, THEPUNCH

    Wata kotun ma'aikata da ke zamanta a Abuja ta umarci likitoci da ke yajin aiki su janye su koma bakin aikinsu.

    Mai shari'a John Targema ya bada wannan umarnin ne a wannan Litinin din.

    Ya kuma ce bayan dogon nazari kan korafe-korafe da bukatar gaggawa ya umarci a yanje wannan yajin aiki.

    Umarnin kotun na zuwa ne adaidai lokacin da kungiyar likitoci masu neman kwarewa a Najeriya ta ce za ta ci gaba da kauracewa asibitoci.

    Wannan kuma na da nasaba da mataki na ci gaba da gudanar da yajin aiki sakamakon gazawar gwamnati wajen biya musu bukatunsu.

    A karshen makon nan ne bangarorin biyu suka yi zama inda aka tashi dutse a hannun riga bisa wata bukata guda daya.

  9. Matar tsohon shugaban Najeriya ta rasu

    IMSG

    Asalin hoton, IMSG

    Rahotanni a Najeriya na cewa Victoria Aguiyi-Ironsi, matar tsohon shugaban ƙasar ta rasu tana da shekara 97.

    Sai dai har yanzu ƴan uwanta basu tabbatar da mutuwar ba.

    Victoria ta kasance matar tsohon shugaban kasa a mulkin soja Manjo-Janar Johnson Aguiyu-Ironsi, wanda ya karɓe mulki bayan juyin mulki a 1966.

    Ya mulki ƙasar na tsawon wata shida, kafin daga bisani a kashe shi a wani yunƙurin kifar da gwamnatinsa da gungun sojoji suka aiwatar.

    Kafin lokacin mutuwarsa, ma'aurata na da yara 8. Ms Aguiyi-Ironsi ba ta sake wani auren ba tun bayan mutuwar mijin.

  10. An samu raguwar yawan mutanen da ake kashewa a Najeriya – Bincike

    A wani rahoto da kamfanin Beacon Consulting mai nazari kan sha’anin tsaro a Najeriya ya fitar, ya ce an samu raguwar kashi 39 cikin dari a watan Yuli na yawan mutanen da ake kashewa a ƙasar, idan aka kwatanta da yawan waɗanda suka mutu a watan Yunin da ya gabata.

    Masana harkar tsaro na ganin cewa wasu sauye-sauye da ake samu a ɓangaren na tsaro sun fara tasiri wajen rage mutanen da suke rasa rayukansu sanadiyyar tashe-tashen hankula a kasar.

    Najeriya na fama da matsalar tsaro musamman a arewacin kasar, abinda ke haifar da rasa rayuka da tagayyara al’umma a kusan kowace rana.

    Ku saurari rahoton Haruna Ibrahim Kakangi:

    Bayanan sautiRahoton Haruna Ibrahim Kakangi:
  11. Shugabar Tanzaniya na shan suka kan muzanta ƴan wasan ƙwallo ƙafa mata

    Shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan

    Shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan ta sha suka saboda yadda ta siffanta 'yan matan kasar masu buga wasan kwallon kafa.

    Wakiliyar BBC ta ce Shugaba Samia - wadda ita ce mace ta farko da ta zama shugabar kasar - ta kwatanta 'yan matan a matsayin masu shafaffen kirji, kuma wadanda suka cika muni, matsalar da ta ce ka iya hana su yin aure.

    Shugabar kasar ta kuma ce ana iya kuskuren wasu 'yan mata 'yan kwallon a ce maza ne. Ta yi waɗannan kalaman ne yayin wani biki da aka shirya na karrama ƙungiyar kwallon kafa ta mata wadanda shekarunsu ba su wuce ashirin da uku ba, da su ka yi nasarar lashe gasar kwallon kafa ta Gabashi da Tsakiyar Afirka.

    Ana kuma sukar Shugaba Samia domin ci gaba da hana ƴan matan da su ka dauki ciki ci gaba da halartar makaranta.

  12. Muna da dubban mayaƙa, in ji masu adawa da Taliban

    NRF

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Mayaƙan NRF sun ce suna so a yi tattaunawar sulhu tukunna kafin a shiga yaƙi

    Wata ƙungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaƙa da ke shirye don fafata yaƙi da Taliban wadda ke iko da mafi yawan Afghanistan.

    BBC ba ta tabbatar da ingancin wannan iƙirari ba, wanda kakakin ƙungiyar National Resistance Front of Afghanistan (NRF) mai suna Ali Nazary ya yi.

    Mista Nazary ya faɗa wa BBC cewa NRF na da "dubban mayaƙa da ke cikin shirin yaƙi" amma za su nemi tattaunawar sulhu tukunna.

    "Idan hakan ta gagara...to ba za mu yarda da kowace irin tsokana ba," a cewarsa.

    Kalaman nasa na zuwa ne bayan Taliban ta ce ta kewaye yankin Panjshir, inda nan ce maɓoyar mayaƙan.

    Shugabannin ƙungiyar sun ce Taliban na ci gaba da tunkarar yankin wanda ke arewa maso yammacin birnin Kabul.

  13. Taliban ta saka wa masu son ci gaba da barin Afghanistan sharaɗi

    Kabul

    Asalin hoton, EPA

    Ƙungiyar Taliban na roƙon 'yan Afghanistan su tsaya domin gina ƙasarsu amma ba za ta hana waɗanda ke son barin ƙasar ba idan suna da cikakkun takardu, kamar yadda kakakin ƙungiyar ya faɗa wa BBC.

    Suhail Shaheen ya ce mutane za su iya ficewa daga ƙasar a jiragen haya ko da wa'adin 31 ga watan Agusta ya wuce - lokacin da dakarun ƙasashen waje za su fice daga ƙasar.

    Ya ce: "Ba za mu dakatar da su ba idan suna da fasfo - za su iya tafiya a jiragen haya a kowane lokaci. Muna son su zauna amma idan suna so za su iya tafiya....idan suna da cikakkun takardu."

    Sai dai ya ce akwai hukunci idan ƙasashen waje suka wuce wa'adin 31 ga Agusta amma bai yi ƙarin bayani kan abin da hakan ke nufi ba, yana mai cewa shugabannin ƙungiyar za su tattauna.

    Ranar Talata ne shugabannin ƙungiyar G7 ta ƙasashe mafiya girman tattalin arziki za su gana ta intanet, inda ake sa ran za su tsawaita wa'adin sakamakon hatsaniyar da ke faruwa a filin jirgi na birnin Kabul.

  14. Ƙungiyar Fulani ta miƙa waɗanda ake zargi da fashi ga 'yan sanda

    Bayanan sautiLatsa hoton sama ku saurari hira da jami'in ƙungiyar Mi Yetti Allah

    A Najeriya, kungiyar Fulani makiyaya ta Mi Yetti Allah a Jihar Taraba ta ce ta mika wa rundunar ‘yan sandan jihar wasu mutum tara da ake zargi da garkuwa da mutane.

    Wannan na zuwa ne sakamakon kiran da Mai Martaba Sarki Muri Alhaji Abbas Tafida ya yi wa Fulani cewa su fallasa duk masu garkuwa da mutane a jihar ta Taraba.

    Sai dai shugaban kwamitin ladaftarwa na kungiyar a jihar, Mafindi Umaru Ɗanburan, ya ce tun kafin sarkin Muri ya yi wannan kiran da ma suna kama wadanda ake zargi da garkuwa da mutane.

  15. An ɗaure tsohon mininsta shekara 12 kan laifin rashawa a Indonesia

    An daure wani tsohon minista a gwamnatin kasar Indonesia tsawon shekara 12 a kurkuku bayan wata kotu ta same shi da laifin karbar cin hanci yayin da yake aikin samar wa iyalai marasa galihu tallafin korona.

    A watan Disamba, 'yan sanda sun binciki Juliari Batubara - wanda a wancan lokacin shi ne ministan jin dadin jama'a - kuma sun gano wasu manyan akwatuna bakwai da wasu kananan jakunkuna uku wadanda aka makare su da dalar Amurka fiye da miliyan ɗaya.

    Wakiliyar BBC ta ce bayan wasu watanni kotun ta gano cewa Mista Batubara ya karbi cin hanci daga wasu 'yan kwangila biyu wadanda aka ba kwangilar raba wa marasa galihu abinci.

    Matsalar cin hanci da rashawa ta girmama a Indonesia. A watan jiya, an daure wani tsohon ministan samar da kifi na kasar a gidan yari shekara biyar bayan, wanda shi ma aka same shi da laifin karbar cin hanci.

  16. Labaran duniya cikin minti ɗaya

    Bayanan sautiMinti Ɗaya da BBC na Rana 23/08/2021
    • Tare da Umar Mikail
    • Wani ƙazamin faɗa ya ɓarke tsakanin wasu ‘yan bindiga da jami’an tsaro a ƙofar shiga filin jirgin Kabul babban birnin Afghanistan.Rundunar sojan kasar Jamus ta ce an kashe wani mai gadi ɗan Afghanistan sannan aka raunata uku a fafatawar da ta ritsa da sojojin Jamus din da na Amurka
    • Mai magana da yawun mayaƙan da ke adawa da Taliban a yankin Panjshir na Afghanistan ya ce ƙungiyarsu za ta nemi tattaunawar sulhu kafin ta shiga yaƙi da Taliban ɗin.Ali Nazary na ƙungiyar National Resistance Front of Afghanistan ya faɗa wa BBC cewa dubban mayaƙa sun taru a ƙarƙashin jagorancin Ahmad Massoud, ɗan shahararren mai adawa da Taliban, Ahmad Shah Massoud kuma a shirye suke su fafata yaki da Taliban
    • A gefe guda kuma, Taliban din ta ce ta sake kama garuruwa uku a arewacin Afghanistan wadanda suka fada hannun mayakan sa-kai a makon da ya gabata.Kungiyoyin mayakan sa-kan sun ƙwace garin Bano da Deh Saleh da Pul e-Hesar da ke yankin Baghlana a matsayin matakin farko na nuna rashin amincewa da Taliban tun bayan da ta kwace iko da birnin Kabul ranar 15 ga watan Agusta
  17. Afghanistan: Taliban ta ce mayakanta sun sake ƙwace garuruwa uku

    Taliban ta kama garuruwa uku a arewacin Afghanistan wadanda suka fada hannun kungiyoyin mayakan sa-kai a makon da ya gabata, a cewar mai magana da yawun ƙungiyar.

    Kungiyoyin mayakan sa-kan sun ƙwace garin Bano da Deh Saleh da Pul e-Hesar da ke yankin Baghlana matsayin matakin farko na rashin amincewa da Taliban tun bayan da ta kwace birnin Kabul ranar 15 ga watan Agusta.

    A ranar Litinin sojojin Taliban sun kwace garuruwan Badakhshan da Takhar da Andarab kusa da tekun Panjshir, a cewar shafin Twitter na mai magana da yawun Taliban Zabihullah Mujahid.

  18. Tsawaita lokacin ficewar dakarun Yamma karya ƙa'ida ce - Taliban

    Mai magana da yawun Taliban, Muhammad Suhail Shaheen, ya yi wata hira da BBC game da rahotannin da ke cewa Birtaniya za ta nemi Amurka ta jinkirta kwashe sojojinta daga Afghanistan har bayan 31 ga watan Agusta.

    "Dole ne dakarun ƙasashen waje su fice a lokacin da suka saka tun farko. Idan ba haka ba kuma an karya ƙa'ida," a cewar Mista Shaheen.

    Sai dai ya ce matakin da ƙungiyar za ta ɗauka a kan saɓa yarjejeniyar kuma yana hannun shugabanninta.

    Har yanzu dubban 'yan Afghanistan na barin ƙasar kafin cikar wa'adin na ƙarshen wata suna masu fargabar abin da ka iya biyo baya idan Taliban ta kafa gwamnati a ƙasar.

    Ƙungiyar dai ta ce tsarin Shari'ar Musulunci za ta gudanar, amma ta ce za a bai wa mata 'yancinsu "kamar yadda Shari'a ta tanada". Sai dai babu tabbas kan abin da hakan ke nufi a aikace.

  19. Afghanistan: Mayaƙa masu adawa da Taliban na son tattaunawa kafin fara yaƙi

    Panjshir

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Ahmad Massoud kenan yake magoya bayansa jawabi a yankin Panjshir na Afghanistan

    Mai magana da yawun mayaƙan da ke adawa da Taliban a yankin Panjshir na Afghanistan ya ce ƙungiyarsu za ta nemi tattaunawa kafin ta shiga yaƙi da Taliban ɗin.

    Ali Nazary na ƙungiyar National Resistance Front of Afghanistan ya faɗa wa BBC cewa dubban mayaƙa sun taru a ƙarƙashin jagorancin Ahmad Massoud, ɗan shahararren mai adawa da Taliban, Ahmad Shah Massoud.

    Nazary ya buƙaci Taliban ta shiga tattaunawa ta gaskiya, yana mai cewa mayaƙan Massoud sun shirya shiga yaƙi.

    "National Resistance Front of Afghanistan ta aminta cewa idan ana neman zaman lafiya wajibi ne a gano bakin zaren matsalolin Afghanistan," in ji shi.

    "Afghanistan ƙasa ce mai al'ummomi daban-daban, tana buƙatar a rarraba iko ta yadda kowa zai samu muƙami."

  20. 'Yan sandan Najeriya sun kama mutum huɗu da zargin fashi

    Bursin

    Asalin hoton, Getty Images

    'Yan sanda a Jihar Delta da ke kudancin Najeriya sun ce sun kama wani gungun mutum huɗu da ake zargi da aikata fashi da kuma shiga ƙungiyar asiri ɗauke da bindigogi.

    Muƙaddashin mai magana da yawun rundunar, Bright Edafe, ya faɗa wa manema labarai cewa kamen ya biyo bayan wani kiran gaggawa da suka samu ne daga wani wanda lamarin mutanen ya ritsa da shi.

    An faɗa wa 'yan sandan cewa wasu 'yan daba na aikata fashi a Titin MTN da ke Ƙaramar Hukumar Sapale, inda nan take DPO na Sapale ya jagoranci tawagarsu zuwa wurin.

    Yayin fafatawa da maharan ne kuma aka kama huɗu daga cikinsu.

    An bayyana sunayensu kamar haka: James Wisdom mai shekara 25, Peter Ayodele shekara 22, Ikolo Micheal shekara 18, Francis Success mai shekara 26.

    Kazalika, an ƙwace mota ƙirar Toyota Lexus daga hannun waɗanda ake zargin.