Ƴan bindiga sun kashe ɗan sanda da ma’aikatan kamfanin mai a Imo
Rahotanni a Najeriya sun ce wasu ƴan bindiga sun kai hari cibiyar wani kamfanin mai a jihar Imo inda suka kashe jami’in ɗan sanda da maka’aikatan kamfanin guda shiga.
Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Imo wanda ya tabbatar wa kamfanin dillacin labaru na Reuters da labarin ya ce rundunarsu ta ɗauki matakai a yankin mai fama da hare-hare.
Kakakin ƴan sandan na jihar Imo Michael Abattam ya ce an kai harin ne a ranar litinin a kamfanin Lee Engineeringda ke aikin gas a yankin Assa.