Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Taliban: 'Shari'ar Musulunci za mu yi'

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau, Nasidi Adamu Yahaya and Umar Mikail

  1. Najeriya: Nan da wata shida za mu cefanar da NNPC - Timipre Sylva

    Ƙaramin Ministan Mai a Najeriya Timipre Sylva ya ce nan da wata shida masu zuwa za su mayar da kamfanin man fetur (NNPC) na 'yan kasuwa.

    Ministan ya bayyana haka ne ranar Talata yayin wani taron manema labarai a Abuja babban birnin ƙasar, kamar yadda Channels TV ta ruwaito.

    Ya ƙara da cewa tuni aka kafa wani kwamati da zai tabbatar da haɗe kamfanin, inda zai koma NNPC Limited.

    Ranar Litinin ne Shugaba Buhari ya sanya wa dokar man fetur hannu mai suna Petroleum Industry Bill (PIB), wadda ta tanadi mayar da NNPC na kasuwanci sannan kuma ta maye gurbin dokar da aka kafa tun 1967.

    Ana sa ran gwamnati ce za ta kula da kamfanin na NNPC Limited wanda zai kasance ƙarƙashin Ma'aikatar Kudi ta Najeriya.

    Mista Silva ya ce duk da cewa sabuwar dokar PIB ta janye maganar ƙayyade farashi a harkar fetur amma tallafin da gwamnati ke bayarwa zai ci gaba har zuwa wani lokaci.

    Nan gaba za a fitar da cikakken tsari game da maganar ƙayyade farashin mai domin rage wa talakawa raɗaɗin abin da zai faru, a cewarsa.

  2. Ko ƙasashen duniya za su amince da gwamnatin Taliban?

    Mai magana da yawun Taliban, Zabihullah Mujahid, ya ce suna tattaunawa domin kafa gwamnati a Afghanistan bayan sun ƙwace iko da ƙasar baki ɗaya, yana mai cewa tsarin Shari'ar Musulunci za su aiwatar.

    To ko yaya sauran ƙasashen duniya suka ji da wannan lamari?

    • Gwamnatin Amurka na ci gaba da tattaunawa da Taliban kan yadda za ta kwashe 'yan ƙasarta da ƙawayenta daga Kabul babban birnn ƙasar. Amma jami'an Amurka sun ce ƙasar ba za ta goyi bayan gwamnatin Taliban ba wadda ta ƙwaci mulki da ƙarfin tsiya. Ya zuwa yanzu Shugaba Biden bai yi magana da wani shugaban ƙasa ba tun bayan da Taliban ta ƙwace Kabul, a cewar mahukunta.
    • Wajibi ne ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) ta tattauna da Taliban domin ta taimaka wa mazauna Afghanistan ko da ba ta amince da gwamnatin ƙungiyar ba, a cewar shugaban harkokin wajen EU. "Ban ce za mu yarda da gwamnatin Taliban ba," in ji Josep Borrell
    • Birtaniya na shirin ƙara yawan aikin tallafin da take bai wa Afghanistan da kashi 10 cikin 100. Sakataren Harkokin Waje Dominic Raab ne ya bayyana hakan amma bai ce ko za su amince da gwamnatin Taliban ɗin ba
    • Ƙungiyar haɗakar sojojin Yamma ta NATO ta dakatar da dukkan tallafi ga Afghanistan saboda tana ƙarƙashin mulkin Taliban. Amma za a ci gaba kai tallafin idan an kafa "gwamnatin haɗin kai", in ji shugaban ƙungiyar, Jens Stoltenberg
    • Canada ba ta da wani shirin amincewa da gwamnatin Taliban, a cewar Firaminista Justin Trudeau, yana mai cewa ƙungiyar ta 'yan ta'adda ce
    • Ministan yaɗa labarai na Pakistan ya ce nan gaba ƙasarsa za ta yanke hukunci kan ko za ta amince da gwamnatin Taliban idan ta gama shawartar ƙawayenta na yanki da kuma na sauran duniya
  3. Har yanzu muna tattaunawa da Taliban - Amurka

    Mai bai wa shugaban Amurka shawara kan tsaro, Jake Sullivan, ya ce ƙasarsa na tattaunawa da Taliban kan ci gaba da aikin kwashe 'yan ƙasarta bayan ƙungiyar ta karɓe iko da ƙasar Aghanistan.

    Mista Sullivan ya yi ta ƙoƙarin kare matakin Amurkar na janyewa daga ƙasar yayin taron manema labarai ɗazu bayan shekara 20 tana yaƙar Taliban.

    Da yake magana kan muatnen da suka rasa rayukansu, Sullivan ya ce dole ne Shugaba Biden ya lura da mutanen da yaƙin ya cinye kafin yanke shawarar ci gaba da zama a Afghanistan ɗin.

    "Idan ana so a dakatar da Taliban to sai an kai dubban dakarun Amurka - ninki baninkin abin da Joe Biden ya tarar," in ji shi.

  4. Uganda ta ce za ta karɓi ƴan gudun hijirar Afghanistan

    Uganda ta ce za ta karɓi ƴan Afghanistan dubu biyu kamar yadda Amurka ta nemi alfarma.

    A ranar Talata kaso na farko mutum 500 za su isa ƙasar. Za a yi masu gwajin korona tare da killace su bayan sun isa ƙasar.

    Uganda za ta kasance ƙasa ta farko daga Afrika da ta karɓi ƴan gudun hijirar Afghanistan.

    Uganda dama ta daɗe tana karɓar ƴan gudun hijira da ke ƙauracewa yaƙi da annoba.

    Kasashen duniya sun yaba ma Uganda kan kyakkyawan tsarin da take da shi da kuma karimci na karbar 'yan gudun hijira

  5. Ra’ayoyin ƴan Borno kan ƴan Boko Haram da ke miƙa wuya

    Ƴan Najeriya musamman ƴan asalin jihar Borno sun bayyana ra’ayoyi mabambanta game da karɓar tubabbun ƴan Boko Haram da rundunar sojin Najeriya ta yi.

    Rundunar Sojin kasa ta Najeriya ta ce wasu karin mayaƙan kungiyoyin Boko Haram da ISWAP 186 sun miƙa wuya. Ta sanar da hakan ne cikin wata sanarwa da kakakinta Burgediya Janar Onyeame Nwachukwu ya fitar.

    Sai dai ra’ayi ya bambanta tsakanin ƴan Najeriya ganin yadda mayaƙan suka yi sanadiyar mutuwar dubban mutane da raba miliyoyi da muhallansu a tsawon shekara goma.

  6. Ku ɗauki makamai don kare kanku daga 'yan fashi - Bello Masari

    Gwamnan Jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ya buƙaci mazauna garuruwan da 'yan bindiga ke yawan kai wa hare-hare da su nemi makamai don kare kan su daga hare-haren.

    Aminu Bello Masari ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin da ya kai ziyarar jaje a Ƙaramar Hukumar Jibia ga iyalan mutum 10 da jami'an hukumar kwastan suka kashe a makon da ya gabata.

    Katsina na cikin jihohin da 'yan bindiga suka fi kashewa tare da yin garkuwa da mutane a arewa maso yamnmacin Najeriya.

    Ranar 11 ga watan Disamba 'yan bindigar da ake zargin 'yan fashin daji ne suka sace ɗalibai daga sakandaren garin Kankara na jihar ta Katsina guda 344, inda suka shafe kwana shida a hannun masu garkuwar.

    "Miƙa wuya da mutane ke yi ga 'yan fashi shi ke jawo ɓarayin su ci gaba da aikata munanan lamura a lokuta da yawa," a cewar Masari cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa Abdu Labaran Malumfashi ya fitar.

    Ya ƙara da cewa "wajibi ne mutane su daina tunanin cewa harkar tsaro ta gwamnati ce ita kaɗai".

    Kazalika, gwamnan ya umarci mutanen yankin da kar su yarda da duk wani ihsani da hukumar kwastan za ta yi musu "har sai an nema wa iyalan waɗanda aka kashe haƙƙinsu".

  7. Muhimman abubuwan da Taliban ta bayyana a taron manema labaranta

    Taliban ta gudanar da taron manema labarai na farko tun bayan da ta karɓe iko da Afghanistan, inda ta taɓo batutuwa da dama. Ga muhimmai daga cikinsu:

    • Ƙungiyar na ƙoƙari tuƙuru don kafa gwamnati kuma "za a sanar da zarar an kammala kafa ta," a cewar Zabihullah Mujahid mai magana da yawun ƙungiyar
    • Ya ce mata za su "taka rawa sosai a al'ummarmu" kuma za a ƙyale su su yi aiki "bisa tsarin shari'armu ta Musulunci", sai dai bai fayyace me hakan ke nufi ba a aikace
    • Da aka tambaye shi game da mutanen da suka yi aiki da gwamnatocin ƙasar waje a matsayin tafinta ko 'yan kwangila, Zabihullah ya ce "babu wanda za a ɗauki fansa a kansa" sannan kuma "ƙungiyar ta yafe wa kowa saboda zaman lafiya da kwanciyar hankalin Afghanistan"
    • Ya ce Taliban za ta mutunta haƙƙin 'yan jarida sannan ya yi alwashin "kafofin yaɗa labarai masu zaman kansu za su ci gaba da ayyukansu ba tare da tsangwama ba"
    • Sai dai ya yi gargaɗin cewa "kar kafofin su sake su yi mana zagon ƙasa"
    • Game da sauran mayaƙan ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi, kakakin ya ce "ba za a yi amfani da Afghanistan a cuci kowa ba"
    • Haka nan ya jaddada cewa mayaƙan Taliban sun so su tsaya a ƙofar gari ne saboda a kammala karɓar gwamnati cikin lumana amma ya zama dole su shiga cikin gari domin tabbatar da tsaro
  8. Taliban ta ƙi fayyace 'yancin mata ma'aikata

    Taron manema labaran da Taliban ta yi ya kammala ba tare da fayyace haƙiƙanin batu ba game da 'yancin mata na yin aiki.

    Har ya kammala jawabinsa, mai magana da yawun ƙungiyar, Zabihullah Mujahid, ya yi ta kauce wa tambayar haƙƙin matan da ke aiki a yanzu.

    Sai dai ya yi ta maimaita cewa za a ba su damar aiki "da ya dace da shari'armu ta Musulunci". Amma bai fayyace me hakan ke nufi ba a aikace.

  9. Taliban: Afghanistan ba za ta zama matattarar mayakan da ke ikirarin jihadi ba

    Gwamnatin Taliban ta ce ba za ta bari mayakan kasashen waje su mayar da Afghanistan matattararsu ba.

    "Babu wanda zai yi amfani da Afghanistan domin kai hari ga wani," a cewar kakakin Taliban Zabihullah Mujahid yayin da aka tambaye shi ko za su bai wa mayakan al-Qaeda mafaka.

    "Muna tabbatar wa kasashen duniya hakan."

    Ya ce "akwai cikakken tsaro a duk fadin kasar nan," yayin da aka tambaye shi game da rahotannin sace mutane da kashe-kashe a yankuna da ke karkashin Taliban.

  10. Taliban: Mata suna da 'yanci a shari'ar Musulunci

    Mai magana da yawun Taliban Zabihullah Mujahid ya ce "Ina son tabbatar wa duniya cewa babu mutumin da za a musgunawa."

    "Ba ma son fuskantar matsala da kasashen duniya. Muna da dama kamar yadda addininmu ya ba mu. Sauran kasashe suna da nasu tsare-tsaren da doka da oda. 'Yan kasar Afghanistan suna da damar yin mulki bisa dokokinsu."

    "[Mu] mun sha alwashin bai wa mata dama a karkashin tsari da dokokin Musulunci," a cewar Mujahid.

    Ya kara da cewa "za su rika yin aiki kafada da kafada da mu. muna son tabbatar wa duniya cewa ba za mu nuna bambanci ba."

  11. Taliban: Mun yafe wa duka wadanda suka yake mu a baya

    Kungiyar Taliban ta bayyana cewa za ta tabbatar kowanne dan kasar Afghanistan ya samu damar walwala tana mai cewa ba ta bukatar abokan gaba.

    A taron manema da take gudanar yanzu haka, mai magana da yawun kungiyar Zabihullah Mujahid, wanda ya bayyana a gaban 'yan jarida a karon farko tun bayan da suka kwace iko, ya ce sun 'yantar da kasar "bayana shekaru 20 na fafutika kuma mun kori 'yan kasashen waje".

    "Wannan lokaci ne na alfahari," in ji shi.

    "Muna son tabbatar da ganin Afghanistan ba ta sake tsunduma cikin yaki ba. Mun yafe wa dukkan mutanen da suka yake mu. Gaba ta zo karshe, " a cewarsa Mujahid.

  12. Labarai da dumi-dumi, Tsohon mataimakin shugaban Afghanistan ya ce shi ne sabon shugaban kasa

    Mataimakin shugaban kasar Afghanistan wanda aka hambarar, Amrullah Saleh, ya yi ikirarin cewa shi ne sabon shugaban rikon kwaryar kasar bayan tserewar Shugaba Ashraf Ghani ranar Lahadi.

    Ya wallafa sakon Tuwita inda ya ce yana ci gaba da zama a kasar kuma yana "tuntubar dukkan shugabanni domin neman goyon bayansu."

    A wani sakon Tuwita da ya wallafa a baya ya ce jikinsa "bai yi sanyi ba" sannan ya yi kira ga 'yan kasar Afghanistan su "shiga shirinsa na bijire wa" 'yan Taliban.

    Tsohon daraktan na hukumar leken asirin Afghanistan, Mr Saleh ya sha alwashi ranar Lahadi cewa "babu wani yanayin" da zai sa ya mika wuya ga Taliban.

  13. Farashin kayan abinci ya ragu a Najeriya - NBS

    Wani rahoton da Hukumar Kididdiga a Najeriya ta fitar ya nuna cewa, an samu raguwar hauhawan farashin kayayyaki a ƙasar a watan Juli.

    Alƙalumman sun nuna cewa an samu raguwar hauhawan farashin kayayyakin da kashi 17.38 a watan Yuli idan aka kwatanta da kashi 17.75 a watan Yuni.

    Rahoton ya kuma nuna cewa farashin kayan abinci ya sauka daga kashi 21.83 a watan Yuni zuwa kashi 21.03 a watan Yuli.

  14. Abin da ya faru a yau a Afghanistan zuwa yanzu

    Idan yanzu kuka shigo shafin, to ga wasu abubuwa da suka faru tun safe a yau a Afghanistan

    • Taliban na daf da fara taronsu na manema labarai na farko tun bayan ƙwace iko da Afghanistan a ranar Lahadi
    • Shugaban Amurka Joe Biden ya kare matakin da ya ɗauka na ficewar ƙasar daga Afghanistan, yana mai cewa duk da "janyewar mai cike da kwamacala" babu wani lokaci da ya fi dacewa na janye dakarun daga Afghanistan.
    • Rahotanni sun ce abubuwa sun lafa a Kabul bayan tataɓurzar daka samu jiya a filin jirgin sama - inda aka ga mutane na ɗane jirgin yaƙin Amurka
    • Ana ta ganin mayaƙan Taliban na bincike a shingayen bincike tare da warware cunkoson ababen hawa
    • Wani shugaban Taliban ya hana mayaƙan shiga gidajen mutane da kuma taɓa motocin ofisoshin diflomasiyya
    • Su kuwa shugabannin Turai sunnuna damuwa kan yiwuwar kwararar 'yan gudun hijira, inda shugaban Faransa Emmanuel Macron yake cewa dole Turai ta "kare kanta daga kwarar mutane ba bisa ka'ida ba.
    • Ministan Ci gaba a Jamus ya ce ƙasar ta dakatar da taimakon agaji zuwa Afghanistan
  15. Taliban ta hana mayaƙanta shiga gidan kowa da taɓa motocin diflomasiyya

    Kungiyar Taliban a Afghanistan ta ce ta umarci dukkan mayakanta ka da su shiga gidan kowa, kuma su guji taba motoci mallakin ofisoshin jakadanci da ke kasar.

    Wannan sanarwar ta fito ne bayan da aka fara samun rahotanni da ke cewa wasu mutane da su kayi shiga irin ta 'yan Taliban sun rika yi wa wasu ofisoshin jakadancin fashi kwana guda da ya gabata.

    'Yan Taliban din kuma sun ce sun yi wa dukkan ma'aikatan gwamnatin kasar afuwa, kuma sun bukaci su koma bakin aikinsu.

    Wakilin BBC ya ce an ga abin mamaki, yayin da wata mai gabatar da shirin talabijin a Kabul ta yi hira da wani jagoran Taliban, abin da a shekarun baya babu wanda zai yi tunanin haka zai taba faruwa musamman a shekarun da Taliban din ke mulkin kasar.

    An bude gidajen biredi da shagunan da ke sayar da magani, kuma motoci sun karu a bisa titunan Kabul, sai dai an daina jin sautin wakoki a wuraren sayar da gahawa da ma cikin motoci.

  16. Dazukan Australiya na barazanar fuskantar gobarar daji

    Masu bincike a Austiraliya sun gano cewa yankunan karkara da ke kusa da dazukan kasar na cikin haɗarin mummunar gobarar daji.

    Masu binciken sun yi amannar cewa akwai alaƙa mai ƙarfi tsakanin shuka iccen katako da ruruwar gobarar daji a kudu maso gabashin kasar.

    Binciken wanda aka gudanar a babbar jami'ar kasa ta Australiyan ya shawarci mahukunta su haramta sana'ar katako kusa da yankunan jama'a.

  17. Amurkawa za su fuskanci matsalar ƙarancin ruwan sha

    Miliyoyin Amurkawa za su fuskanci matsalar rashin ruwa daga shekara mai zuwa bayan ayyana ƙarancinsa a babbar madatsar ruwa ta tafkin Mead da ke bayar da ruwan ga jihohin kudu maso yammacin kasar da fari ya yi wa katutu.

    Jihohin da ake sa ran matsalar za ta shafa sun hada da California da Colorado da Nevada da Oklahoma da Texas da Arizona da Utah.

    Shi dai tafkin Mead mafi girma a Amurka na raguwa cikin shekaru ashirin da suka gabata, kamar yadda ake gani a Kogin Colorado.

    Mahukunta na danganta lamarin da sauyin yanayi.

  18. Buhari zai gana da shugabannin tsaro na Najeriya

    Shugabannin Najeriya Muhammadu Buhari zai gana da shugabannin tsaro a fadarsa a ranar Alhamis.

    Sanarwar da fadar shugaban na Najeriya ta fitar ta ce Buhari wanda ya dawo daga London a ranar Juma’a zai gana da shugabannin tsaron ne domin tsara tsare-tsaren kawo ƙarshen ƙalubalen tsaro da ke gabansu.

    Sanarwar ta ce jami’an tsaron ƙasar sun ƙara ƙaimi wajen yaƙi da masu tayar da ƙayar baya da ƴan fashin daji da sauran masu aikata laifuka da suka addabi ƙasar waɗanda hakan ke sa suke miƙa wuya.

    Ganawar ta ranar Alhamis a cewar sanarwar, ta shafi sanar da shugaban ƙasa kan ci gaban da aka samu.

  19. Yadda ɗaruruwan ƴan Afghanistan suka cika maƙil a cikin jirgin Amurka

    Wani hoto mai ban mamaki ya nuna yadda mutane da dama a Afghanistan ke yunƙurin ficewa daga ƙasar.

    Ɗaruruwan ƴan Afghanistan sun yi ruguguwar shiga jirgin na sojin Amurka C-17 a ranar Lahadi wanda ya tashi daga Kabul zuwa Qatar, sa’o’i bayan Taliban ta ƙwace babban birnin Afghanistan.

    Maimakon korarsu, matuƙan jirgin sun yanke shawarar tafiya, kamar yadda shafin labarai na ma’aikatar tsaron Amurka ya bayyana.

    Kusan mutum 640 aka bayyana ke cikin jirgin – adadin mutane mafi yawa da jirgin ya taɓa ɗauka.

    Wani hoton bidiyo a ranar Litinin ya nuna yadda mutane ke gudu a titin jirgin sama yayin da yake ƙoƙarin cirawa sama. Rahotanni sun ce mutane uku sun mutu waɗanda suka maƙale a jirgin.

  20. Ƴan bindiga sun kashe mutum 37 a Nijar

    Rahotanni sun ce fararen hula 37 ne aka kashe a yankin yammacin Nijar a hare-haren da ƴan bindiga masu da’awar jihadi da ake tunanin daga Mali suka tsallako suka kai.

    Kamfanin dillacin labaru na AFP ya ce majiyoyi daga yankin da suka tabbatar da harin a yau Talata, sun ce ƴan bindigar sun abka ƙauyen Darey-Daye da ke cikin yankin Tillaberi saman babura a yammacin Litinin suka buɗe wa mutane da ke aiki a gona wuta.

    Kuma cikin waɗanda aka kashe sun ƙunshi mata da ƙananan yara 13, kamar yadda wani jami’i a yankin ta tabbatarwa AFP.