Sudan na shirin zama mamba a Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya
Majalisar ministocin Sudan ta amince da wani ƙudiri da zai sanya ƙasar cikin mambobin ƙasashen na Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC).
An amince da ƙudirin ne yayin da ake shirin yin wata ganawa tsakanin ministoci da kuma tawagar shugabannin ƙasar.
"Adalci da gwamnati mai gaskiya ne ƙashin bayan sabuwar Sudan, wadda ke bin dokoki sau da ƙafa da muke muradin cimmawa," a cewar Mista Hamdok.
Lamarin na ƙara matso da matakin Sudan kusa na miƙa waɗanda ake zargi da aikata laifukan yaƙi a yankin Darfur, ciki har da tsohon Shugaba Omar al-Bashir.