Cutar amai da gudawa ta hallaka mutum 40 a Jigawa
Hukumomi a jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya, sun tabbatar da mutuwar fiye da mutum 40, sakamakon barkewar cutar amai da gudawa a sassan jihar.
Cutar dai ta bulla ne a kananan hukumomi tara ciki har da Dutse, babban birnin jihar, bayan da wasu mutane suka sha ruwan da ya gurɓata, inda fiye da mutum dubu daya suka kamu da cutar.
Dr Salisu Mu’azu, shi ne babban sakatare a ma’aikatar lafiya ta jihar Jigawa, kuma ta waya ya yi wa Zahraddeen Lawan karin bayani.
Ku latsa lasifikar ƙasa don sauraren hirar: