An kama ɗan sandan Najeriya bayan ya yi harbe-harbe kan mai tsautsayi

Wannan shafin na kawo muku rahotanni na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. 'Yan fashin daji sun kashe mutum 10 a Jihar Kaduna

    'Yan fashin daji

    Wasu 'yan bindiga da ake zargin 'yan fashin daji ne sun kashe aƙalla mutum 10 a yankin Zangon Kataf na Jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya.

    Mazauna yankin sun faɗa wa BBC cewa maharan sun shiga ƙuyukan ne da yawansu ranar Juma'a, inda suka kunna wa gidaje wuta tare da raunata mutane da dama.

    Kwamishinan Tsaro, Samuel Aruwan, ya tabbatar da faruwar hare-haren kuma ya ce jami'an tsaro na binciken wasu matasa biyar da suka ɓata a garin Kafanchan.

    A ranar Litinin da ta gabata ne 'yan fashin suka sako Sarkin Kajuru Alhaji Alhassan Adamu shi kaɗai bayan sun sace shi tare da wasu 13 a gidansa.

    Har yanzu akwai ɗaliban sakandare kusan 120 a hannun 'yan fashin waɗanda suka sace a makarantar Bethel Baptist a Kadunan a farkon watan Yuli.

  2. An kama ɗan sandan Najeriya bayan ya yi harbe-harbe kan mai tsautsayi

    Najeriya

    Asalin hoton, AFP

    Rundunar 'yan sandan JIhar Abia ta tsare wani ɗan sanda mai muƙamin mataimakin sufuritanda bayan ya zaro bindiga tare da yin harbe-harbe a sama.

    Ifeanyi Henry ya fito da bindiga tare da hawa kan titi yana cin zarafin mata da ƙananan yara da 'yan kasuwar yankin Okwu na Uka da ke birnin Aba da ke kusa da ofishinsu, a cewar rahoton Daily Trust.

    Rahoton ya ce jami'in ya fara aikata hakan ne da misalin ƙarfe 7:00 na yammacin Asabar.

    Wasu da Daily Trust ta zanta da su a wurin sun bayyana cewa ɗan sandan ya lalata kayan wata mata mai sayar da kayayyaki a kusa da ofishin sannan ya lakaɗa mata duka. Shaidun sun yi zargin cewa da alama a bige yake sakamakon ƙwaya da ya sha.

    "Ina yin tur da abin da ɗan sandan ya aikata kuma ina tabbatar muku cewa yana tsare yanzu haka da zummar hukunta shi," in ji SP Geoffrey Ogbonna, kakakin 'yan sandan Abia.

    "Rundunar 'yan sandan Najeriya mai ɗa'a ce. Haka nan akwai ƙa'idojin aiki da suka tanadi hukunta duk wani jami'i komai girman muƙaminsa."

    Sai dai ba a bayyana ko ɗan sandan ya harbi wani ba, yayin da aka kai waɗanda ya jikkata asibiti.

  3. Alhazai sun isa Mina a ranar Tarwiya

    Hajji

    Asalin hoton, @CGCSaudi

    Wasu daga cikin alhazai 60,000 sun bar Masallacin Harami, inda suka isa Mina a matsayin wani ɓangare na aikin Hajjin 1442.

    Mahajjatan sun isa ne a yau Lahadi 8 ga watan Zul Hijjah (18 ga Yuli), inda za su shafe yinin na yau a can wanda ake kira Tarwiya.

    A gobe Litinin ne kuma za a tsayuwar Arafa, wanda shi ne mafi girman rukuni na ibadar Hajjin da Musulmai ke aiwatarwa a duk shekara.

    Hajji

    Asalin hoton, @CGCSaudi

    Hajji

    Asalin hoton, @CGCSaudi

  4. Tattaunawa a rana ta biyu tsakanin Taliban da gwamnatin Afghanistan

    Taliban

    Asalin hoton, Reuters

    A rana ta biyu, ana ci gaba da tattaunawar sulhu a Qatar, yayin da tashin hankali ke ci gaba da ƙazanta tsakanin gwamnatin Afghanistan da mayaƙan Taliban.

    Wakiliyar BBC ta ce dubban mutane na ci gaba da tserewa karuwar rikici saboda da fargaba da yunwa da kuma zafin rana da tsananinsa ya kai maki 45.

    Ƙaramin Ministan Zaman Lafiya na Afghanistan Sayed Mansour Naderi ya shaida wa BBC cewa suna fatan ɓangarorin biyu za su fayyace ra'ayoyinsu kan muhimman batutuwan da za su taimaka wajen tsara jadawalin hanyar siyasa don kawo karshen yakin.

    Mataimakin shugaban ƙungiyar Taliban, Abdul Ghani, ya yi magana game da buƙatar samar da aminci yayin da damuwa ke daɗa ƙaruwa game da makomar siyasar Afghanistan.

  5. Hatsarin mota ya kashe mutum 14 a Jihar Osun

    Hatsarin mota

    Asalin hoton, FRSC

    Hukumar kiyaye haɗura a Najeriya ta Federal Road Safety Corps (FRSC) a Jihar Osun ta ce mutum 14 sun rasu sakamakon wani hatsarin mota a yammacin Asabar.

    Kwamandan FRSC a Osun, Paul Okpe, shi ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa a Osogbo ranar Lahadi, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito.

    Sanarwar ta ce hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:40 a kan babbar hanyar Ipetu-Ijesa–Ilesa, inda maza biyar suka mutu da mata huɗu da yara shida.

    Ya ce hatsarin ya ritsa ne da mutum 18 jumilla, inda aka ruga da mata huɗu da suka tsira zuwa asibiti da ke kusa.

    "An kai gawar mutum 14 mutuware sannan an buɗe titin domin guje wa cunkoso a kan babbar hanyar," in ji shi.

  6. Gwamnatin Ghana ta kashe kaji 4,500 saboda murar tsuntsaye

    Kaji

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Ghana ta kashe kaji 4,500 tare da hana zriga-zirga da su bayan an samu kusan 6,000 da suka mutu sakamakon murar tsuntsaye mai suna H5N1.

    Shugaban ma'aikatar dabbobi ta ƙasar ya fada wa Reuters cewa kajin sun fito ne daga gona bakwai da ke Tsakiyar Birnin Accra da kuma Yankunan Volta.

    Patrick Abakeh ya ƙara da cewa yanzu haka an dakatar da zirga-zrigar kaji a yankunan.

    Kazalika, Ghana ta dakatar da shigar da kaji ƙasar daga ƙasashen Nijar da Najeriya da Togo da Burkina Faso da Mauritania da Senegal a matsayin matakin ko-ta-kwana.

    Wannan ne karo na huɗu da annobar murar tsuntsayen take ɓarkewa a Ghana tun 2015.

  7. Mazauna Turai na tsaftace muhallansu bayan ambaliya ta kashe mutum fiye da 170

    Turai

    Asalin hoton, EPA

    A Nahiyar Turai, mazauna wasu yankunan Jamus da Belgium da mummunar ambaliya ta fi shafa sun fara gagarumin aikin tsaftace muhallansu, yayin da ruwan sama ya fara lafawa.

    Ma'aikatan agaji da na sa-kai na ci gaba da neman waɗanda suka bata.

    Mahukunta sun ce an samu gawar mutum fiye da 170 kuma huɗu daga cikin wadanda suka mutu ma’aikatan kashe gobara ne na Jamus.

    "Waɗannan yankuna ne da ke zaune lafiya amma ga shi yanzu suna rayuwa cikin mummunan bala'i, na kadu da samun rahoton wuraren da yanzu haka ruwa ya shafe baki daya," a cewar Shugabar Gwamnatin Jamust Angela Markel.

    An kwashe mutum fiye da 400,000 da ke zaune a yankunan gangare tun da farko don tseratar da rayukansu.

  8. Kwamatin yaƙi da korona ya shawarci masarautar Kano ta soke Hawan Sallah

    Boss Mustapha

    Asalin hoton, PSC

    Kwamatin yaƙi da cutar korona na Gwamnatin Tarayyar Najeriya ya saka jiha shida da kuma Abuja cikin mafiya haɗarin yaɗuwar cutar sannan ya shawarce su da su soke bukukuwan Babbar Sallah.

    Shugaban kwamatin Presidential Steering Committee (PSC) kuma Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a daren Asabar.

    Ya zayyana jihohin kamar haka: Legas, Kano, Kaduna, Oyo, Rivers, Filato da Abuja. Mista Mustapha ya ce shi kansa fitar da jerin sunayen mataki ne na yaƙi da yaɗuwar cutar.

    "Waɗannan matakan na da muhimmanci sosai yayin da muke ganin ƙaruwar masu kamuwa da cutar a Najeriya," a cewarsa.

    "Kwamatin PSC na taya Musulmai murnar Eid-el-Kabir (Idin Babbar Sallah). Sai dai yana shawartar gwamnatocin jiha da shugabannin addini da su san cewa akwai yiwuwar yaɗuwar cutar duk sanda aka tara dubban jama'a."

    Saboda haka ne kwamatin ya shawarci jihohin da su soke Hawan Sallah sannan kuma a yi Sallar Idi a masallatan Juma'a.

    Matakin ya biyo bayan ɓullar nau'in cutar mai suna Delta a jihohin ƙasar da kuma ƙaruwar masu kamuwa da ita da waɗanda ake kwantarwa a asibiti.

  9. An harbe mutum huɗu a wajen filin wasa a Amurka

    'Yan sandan Amurka

    Asalin hoton, Getty Images

    'Yan sanda a birnin Washington DC na Amurka sun ce an harbe mutum huɗu a wajen babban filin wasan kwallon Baseball da ke birnin.

    Lamarin ya haifar da soke wasan da ake tsaka da gudanarwa tsakanin tawagar babban birnin na Amurka da takwarorinsu na San Diego Padres.

    'Yan sanda sun ce an kai mutum biyu asibiti ba tare da mummunan rauni ba sannan wasu biyu sun kai kan su asibitin.

    Suka ƙara a cewa da alama babu wata fargaba a yanzu.

  10. Mutum 123 sun kamu da korona a Najeriya ranar Asabar

    Korona

    Asalin hoton, Getty Images

    Mutum 123 ne suka kamu da cutar korona a Najeriya ranar Asabar, a cewar hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a ƙasar.

    Adadin na wannan lokaci ya fi yawa a Legas inda aka samu mutum 70, da kuma jihar Akwa Ibom mai mutum 18, sai Ogun da mutum 10.

    Sauran su ne: Oyo mai takwas, Rivers takwas, Ekiti huɗu, birnin Abuja mai huɗu, da kuma Jihar Bayelsa mai mutum ɗaya.

    Yanzu a jimillance mutum 169,329 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a faɗin Najeriya, inda ta kashe 2,126 daga cikinsu.

    Sai mutum 164,672 daga cikin jumillar adadin sun warke.

  11. Barka

    Umar Mikail ne ke muku maraba da shigowa shafinmu na labarai kai-tsaye.

    Za mu kawo rahotannin wasu daga cikin abubuwan da ke faruwa a sassan duniya har zuwa dare.