Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Mata masu ciki sun mutu a turmutsutsun karbar abinci a Borno

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da sauran kasashen duniya

Rahoto kai-tsaye

Fauziyya Kabir Tukur and Buhari Muhammad Fagge

  1. Shugaban Mali da aka sauke ya yi barazanar kai shugaban riko kotu

    Lauyan shugaban Mali na mika mulki da aka tsige, Bah Ndaw da Firai Minista Moctar Ouane ya yi barazanar kai shugaban riko na yanzu Kanal Assimi Goita kotu bisa tsare tsoffin jami'an na gwamnati, kamar yadda gidan rediyon faransa, RFI ya ruwaito.

    A cewar shafin inatent na Mali, kungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International ta yi kira da gaggauta sakin tsoffin shugaban.

    An tsare Bah Ndaw da Moctar Ouane a sansanin sojoji na Kati a wajen Bamako biyo bayan juyin mulkin da aka yi ranar 24 ga watan Mayu sannan daga baya aka yi masu daurin talala.

    Wasu manyan kungiyoyin kasa da kasa ciki har da majalisar Dinkin Duniya da Hukumar Kasashen Afrika sun yi kira da a sake su.

  2. Ambaliyar ruwa ta hallaka mutum shida a Jamus

    A ƙalla mutum shida ne suka mutu sannan da dama suka ɓata sakamakon ambaliyar ruwa a yammacin Jamus, a cewar ƴan sanda.

    Abin ya fi ƙamari a jihar Rhineland-Palatinate, inda kusan mutum 50 suka ɗane kan rufin kwankukan gidaje don neman mafaka suna jiran a ceto su.

    Har yanzu ba a ga gwamman mutane ba a yankin Eufel bayan da gidaje da dama suka rushe, a cewar kafar yaɗa labarai ta SWR.

    Yawanci ambaliyar ta faru ne a yayin da Kogin Ahr ya tumbatsa.

    Shugabar jihar Rhineland-Palatinate, Malu Dreyer, ta bayyana yanayin da cewa "babban bala'i" ne.

    Ta ce: "Mutane da dama sun rasu, wasu sun ɓata ko suna cikin haɗari. Dukkan ma'aikatan agajinmu ne aiki kai da fata don ceto rayuwar mutane."

    An rufe makarantu, sannan an rufe hanyoyin jiragen ƙasa a faɗin ƙasar.

    Kusan gidaje 25 na cikin haɗarin rushewa a kusa da garin Adenau a yankin Eifel.

  3. Shugaba Buhari na ziyara a Kano

    Nan gaba a yau Alhamis ne ake sa ran Shugaban Najeriya Muhammad Buhari zai ziyarci jihar Kano da ke arewacin kasar domin kaddamar da ginin sabon layin dogo daga jihar zuwa Kaduna.

    Ana sa ran sabon layin dogon zai hade da na jihar Kaduna zuwa Abuja, da wanda ya taso daga Abuja zuwa Lagos.

    Bayan ya kammala ƙaddamar da aikin zai wuce a mota zuwa ƙaddamar da gadar sama da ta ƙasa da ke dangi a kan titin Kano zuwa Zaria, sannan ya je gidan Sarkin Kano, daga bisani sai ya koma Abuja.

    Ga wasu hotuna na layin dogon Kano na yanzu:

  4. Amnesty International ta yi Allah wadai da cin zarafin bakin haure a Libya

    Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International, ta yi Allah wadai da abin da ta kira hadin bakin da kasashen Turai ke yi wajen aiwatar da mummunan cin zarafi a kan bakin hauren da ake tursasawa komawa Libya.

    Wani rahoto da kungiyar ta fitar ya nuna cewa yanayin da bakin hauren ke ciki na kara tabarbarewa, kana ana azabtar da su, da tilasta musu aikin karfi,da kuma cin zarafinsu ta hanyar lalata.

    Alkaluman Majalisar Dinkin Duniya dai sun ce masu tsaron gabar ruwan Libya sun mayar da fiye da mutane dubu goma sha uku zuwa kasar a watanni shida na farkon wannan shekarar.

  5. Najeriya za ta fara aiki da butumbutumi don yaki da matsalolin tsaro

    Majalisar Dattijan Najeriya ta ce Ma'aikatar Sadarwa ta kafa wata cibiya da za ta rika aiki da butumbutumi da basirar na'ura don yaki da matsalolin tsaro a kasar.

    Najeriya dai na ci gaba da fama da matsalolin tsaro da suka hada da garkuwa da mutane don kudin fansa da hare-haren 'yan bindiga musamman a arewacin kasar da ma ayyukan masu ikirarin jihadi a arewa maso gabashin kasar.

    Kawo yanzu, sama da dalibai 1,000 ne aka sace daga makarantu a arewacin Najeriya tun daga watan Disamban 2020.

  6. Majalisar Dinkin Duniya ta ce halin da ake ciki a Afghanistan ya yi matukar muni

    Wani babban jami'in Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana halin da ake ciki a Afghanistan a matsayin wani mummunan bala'i da tashin hankali ya haifar.

    Dakta Ramiz Alak-barov wanda shi ne mai kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Afghanistan - ya ce kasar bata taba samun kanta cikin wani lokaci da take bukatar dauki kamar yanzu ba.

    Dr Alak-Barov ya ce halin jin kan da ke ci gaba da munancewa a kan idanunmu babban al'amari ne da yaki ya haifar, da kuma halin da mutane ke shiga sakamakon raba su da gidajensu.

    A halin da ake ciki dai kasa da kashi arba'in cikin dari kacal, na dala biliyan daya da miliyan uku da Majalisar Dinkin Duniya ta nema don agazawa Afghanistan ne aka iya yin karo-karonsu.

  7. Wani mutum a Kenya ya amsa laifin kashe yara 13

    Wani mutum a Kenya ya amsa laifin kashe yara 13.

    An kama Masten Milimo Wanjala mai shekara 20 ranar Laraba bayan bincike kan kisan wasu yara biyu kwanan nan.

    An gano gawarwakin yaran ne a unguwar Kabete a kusa da Nairobi, babban birnin kasar.

    Wanjala ya amsa laifin kashe yaran biyu da ma wasu tara da shekarunsu ke tsakanin 12 zuwa 13 sannan ya yi wa masu bincike bayanin inda ya gudanar da kisan.

    'Yan sanda na gudanar da bincike don gano gawarwakin yaran.

    KIsan daya daga cikin yaran ya janyo zanga-zanga a unguwar Kumukuywa a yammacin Kenya.

    A lokacin, masu zanga-zanga sun kona gidan wani mutum da aka yi zargin ya kashe yaron.

    A yanzu, za a gurfanar da Masten Wanjala bisa laifin kisan duka yaran.

  8. Budewa

    Barkanku da kasancewa da mu a wannan shafin da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.