Ana taro kan yadda za a murkushe ISWAP
A ranar Litinin ne Ministocin harkokin waje daga sama da kasashe 40 za su yi wata ganawa a Roma, babban birnin Italiya domin tattauna karuwar barazanar ayyukan kungiyar IS a Afirka.
Yayin da IS ta fuskanci koma-baya a Syria da Iraki, tasirin kungiyar mai ikirarin Jihadi na ci gaba da karuwa a sassan nahiyar Afirka.
Burtaniya za ta yi alkawarin samar da karin kudaden yaki da reshen kungiyar ta IS a Yammacin Afirka da ke da alhakin tada zaune tsaye a Chadi da Kamaru da kuma Najeriya.