Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Buhari zai tafi London don duba lafiyarsa

Wannan shafin na kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Imam Saleh

  1. Ƙarin mutum 44 sun kamu da korona a Najeriya

    Mutum 44 sun kamu da cutar korona a Najeriya ranar Laraba, a cewar hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a ƙasar.

    Alƙaluman da hukumar ta wallafa sun nuna cewa daga jihohi huɗu ne har da Abuja aka samu sabbin kamuwar sannan kuma babu wanda ya rasa ransa.

    Jihoihin su ne Legas mai mutum 32, da Rivers mai takwas, sai kuma Abuja da Filato masu biyu-biyu kowaccensu.

    NCDC ta ce ya zuwa yanzu mutum 167,375 ne aka tabbatar sun kamu da cutar sannan ta kashe 2,118. Kazalika, an sallami mutum 163,917 bayan sun warke.

    Annobar korona ta ɓulla Najeriya ne a watan Fabarirun 2020, wata uku kenan bayan da aka gano ta a ƙasar China.

  2. Gafaranku dai

    Masu bibiyarmu a wannan shafi barkanmu da hantsin Alhamis.

    Umar Mikail ne ke muku fatan kun shigo shafin labarai kai-tsaye lafiya, wanda zai dinga kawo rahotannin abubuwan da ke faruwa daga sassan duniya.

    Sai dai za mu fi mayar da hakali ne kan Najeriya da Nijar da maƙotansu.