Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Buhari zai tafi London don duba lafiyarsa

Wannan shafin na kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Imam Saleh

  1. Rufewa

      • Marubuci, Imam Saleh
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multimedia Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu ta wannan shafi a nan za mu yi sallama da ku a wannan rana ta Alhamis, sai dai za mu sake dawowa gobe Juma'a domin ci gaba da kawo muku labaran duniya kai tsaye.

    Za ku iya dubawa ƙasa, don samun labarai masu jan hankali da muka wallafa tun daga safiyar wannan rana har kawo yanzu.

    Imam Saleh ke cewa mu kwana lafiya, daga nan sashen Hausa na BBC.

  2. Matsalar tsaro ta kusa zama tarihi a Najeriya - Osinbajo

    Mataimakin shugaban Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo, ya ce matsalar tsaron da kasar ke fama da ita na daf da zama tarihi.

    Yana magana ne lokacin da ya karbi bakuncin wani mai rike da sarautar gargajiya, wato Oluyin na Ekiti a Abuja, inda ya ce shugaba Muhammadu Buhari ya nemi majalisar dokoki ta amince da kwarya kwaryar kasafin daya mika mata na kusan dala biyan 900, domin zuba su a harkar tsaron kasar.

    Sanarwar da mai magana da yawun mataimakin shugaban ƙasar Laolo Akande ya fitar, ta ambato yana cewa tuni shugaban ya kafa wani kwamiti da zai duba bukatun dukkanin hukumomin tsaron Najeriya domin a biya musu, ta yadda za a murkushe matsalar cikin gaggawa.

    Tuni majalisar ta amince da buƙatar kashe kudaden.

  3. Buhari ya raba wa tsafffin 'yan wasan Super Eagles gidaje

    Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar da ba wa tsafaffin 'yan wasan kungiyar kwallon kafa Najeriya wato Super Eagles da suka lashe gasar cin kofin Nahiyar Afrika ta 1994 kyautar gidaje masu dakuna uku-uku.

    Shugaban ya ce ya cika alkawarin da ya yi wa 'yan wasan ne saboda yadda suka jajirce a gasar da aka yi a Tunusia.

    A cewarsa ''Wadannan 'yan wasa sun fito da darajar Najeriya, kuma sun sa muna alfahari da ƙasarmu, don haka abun da za mu yi musu kawai shine cika alkawarin da muka yi musu''

    Za a basu gidajen ne a duk inda suka zaba.

  4. Yan sanda sun tabbatar da sace mutane 12 a Kaduna

    Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta tabbatar da sace mutane 12 da wasu gungun yan bindiga suka yi a garin Kachia da ke jihar Kaduna.

    Mai magana da yawun rundunar a jihar ASP Muhammed Jalige ya tabbatar da sace mutanen yayin zantawa da jaridar Vanguard.

    Ya ce ''A ranar 23 ga watan Yuni, jiya kenan, rundunarsu ta samu wani rahoto mara dadi daga Kachia, cewa da daddare wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba, dauke da muggan makamai sun mamaye mahadar Awon / Mothercat a karamar hukumar inda suka fara harbin kan mai uwa da wabi.

    Ya ce, da samun wannan bayanin, hadin guiwar 'yan sanda da sojoji da kuma 'yan banga suka durfafi wajen da nufin tunkarar yan bindigar, amma sai suka tarar sun yi wa mutane hudu rauni, yayin da kuma suka kashe wani mai suna Hamisu Mikailu, mai shekaru 40 a duniya.

    Ya ce sun kuma yi awon gaba da mutane 12, yayin da su kuma wadanda aka raunata ke ci gaba da karbar magani a asibiti.

  5. Arewa24 na bikin cika shekaru 7 da fara watsa shirye shirye

    Kafar talaijin ɗin Arewa24 da ke haska shirye shiryen nishadantarwa da ilimantarwa na bikin cikarta shekaru 7 cif cif da fara watsa shirye shirye.

    Albarkacin cika lokacin kafar ta yi alkawarin bijiro da sabbin shirye shiryen wasan kwaikwayo, da kuma shirin Tattauna batutuwa na mata zalla, harma da na kananan yara don ilmantar da su da kuma nishadantar da su.

    Arewa24 wadda abokiyar ƙawancen BBC Hausa ce a yankin Afrika ta yamma, ta ce za ta ci gaba da haska fina-finan nan nata biyu da suka samu shiga a wajen jama'a, da suka hadar da Kwana Casa'in da kuma Dadin Kowa

    An kafa tashar ne a shekarar 2014, da zummar samar da managartan shirye-shiryen nishadantarwa na Hausa da za su bunkasa harshen da kuma al'adar Malam Bahaushe.

  6. Sarkin Katsinan Maradi ya rasu

    Mai Martaba Sarkin Katsinar Maradi Sultan Maremawa Alhaji Ali Zaki ya rasu, yana da shekara 83 a duniya

    Sarkin ya rasu ne yau Alhamis da rana a wani babban asibiti da ake kira Hopital de Reference da ke birnin Katsinar Maradin na Jumhuriyar Nijar.

    Kafin rasuwarsa. ya jima yana fama da rashin lafiya.

    Ya bar mace daya da ‘ya‘ya 7 maza da mata.

    Ya zama sarkin Katsinar Maradi ne sakamakon rasuwar Sarkin wancan lokaci ,marigayi Alhaji Mahamane Sani wanda ake kira da Bouzou Dan Zambadi.

    Sarki Ali Zaki Maremawa ya hau kan karagar saurautar Katsinar Maradi a ranar 1 ga watan Oktoban shekara ta 2005.

  7. Labarai da dumi-dumi, Buhari zai tafi London don duba lafiyarsa

    Fadar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ta ce shugaban zai tafi Landan gobe Juma'a don duba lafiyarsa.

    Mai taimakawa shugaba Buhari kan harkokin yaɗa labarai Femi Adesina ne ya sanar da hakan cikin wata gajeruwar sanarwa da ya fitar yau Alhamis.

    Ya ce ana sa ran shugaban zai koma gida Najeriya a mako na biyu na watan Yuli mai kamawa.

  8. Barcelona ta aika wa Messi wasiƙa

    Barcelona ta aika wa dan wasanta kuma kyaftin din kungiyar Lionel Messi wasikar taya shi murnar zagayowar ranar haihuwarsa.

    Messi ya cika shekaru 34 a ranar Alhamis, a dai-dai lokacin da aka kasa tantance makomarsa a kungiyar. Kungiyar.

    Barcelona ta yi ta wallafa hotuna da bidiyoyin zakakurin dan wasan a shafukanta na sada zumunta, to sai dai hakan bai zo da mamaki ba, domin Messi ne babban dan wasan kungiyar a tsawon lokaci, don haka dole ne su yi mararin faranta masa a wannan rana, ko don ya sake rattaba musu hannu.

    Shine dan wasan da ya fi kowa zura kwallaye a raga a kungiyar kuma ya buga wasanni da yawa fiye da kowane dan wasa, sannan kuma ya lashe Ballon d’Or sau shida a kungiyar.

  9. Za a daina tallan abinci mai sa ƙiba a Birtaniya

    Za a dakatar da tallace-tallacen abincin da ake ganin yana yi wa lafiyar mutane illa a gidan talabijin na Birtaniya karkashin shirin da gwamnati ta sanar domin rage yawan ƙiba tsakanin yara.

    Matakin zai kuma shafi wasu tallacen-tallacen intanet da kuna talabijin da ake yi kafin karfe 9:00 na dare.

    Matakin zai shafi abinci mai maiƙo sosai da gishiri da kuma sikari.

    Ƙungiyar masu talla ta nuna rashin jin dadinta kan haramcin, sai dai Ministar Kiwon Lafiyar Jo Churchil ta ce wannan zai taimaka wajen rage yawan maiƙo a abincin da ake ci a kasar.

    An yi kiyasin cewa a cikin yara uku da ke barin makarantar firamare a Biraniya ɗaya daga cikinsu mai ƙiba ne.

  10. Yara miliyan ɗaya ka iya mutuwa a Najeriya nan da 2030

    Shirin raya kasashe na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) wato UNDP ya ce adadin ƙananan yara da za su mutu zai iya kaiwa miliyan ɗaya nan da shekara ta 2030 idan ba a magance matsalar ba.

    UNDP ta ce yara 170 ne suka yi ta mutuwa a kowace rana a Najeriya a shekarar 2020 da ta wuce sakamakon rikicin Boko Haram da ake fama da shi a arewa maso gabashin kasar.

    A cewar rahoton, yawan kananan yaran da ke mutuwa a yankin zai iya kaiwa 240 a kowace rana nan da zuwa shekara ta 2030.

    Lamarin kamar yadda shirin na raya ƙasashe na MDD ya bayyana, ya fi shafar yara masu rauni `yan kasa da shekara biyar, waɗanda ke fama da yunwa da kuma cutuka sakamakon karancin ruwan sha mai inganci.

    Yanayin rikici, musamman yadda ya ki ci ya ki cinyewa, sannan kuma ake mirginawa da shi daga wata shekara zuwa wata, yana mummunan tasiri a kan kananan al'umma musamman yara.

  11. Mata masu yin gurasa a Kano za su fara yajin aiki

    Kungiyar mata masu yin gurasa a Kano sun yi barazanar shiga yajin aikin a ranar Alhamis ɗin mako mai zuwa sakamakon tashin farashin fulawa a kasuwannin jihar.

    Masu yin gurasar sun zargi kamfanonin IRS da Bua da yi musu ƙarin farashin fulawar, inda suke sayen ta a kan N16,900.

    Wakilin BBC Kano Khalifa Dokaji ya ce wannan na zuwa ne mako guda da janye yajin aikin jan kunne na kwanki huɗu da suka shiga a makon da ya gabata.

    Latsa hoton ƙasa ku saurari rahoton Dokaji daga Kano:

  12. Ana ci gaba da ceto mutanen da gini ya binne a Amurka

    Ma’aikatan ceto na neman masu sauran numfashi a cikin baraguzan wani bene mai hawa goma sha biyu da wani bangarensa ya ruguje a garin Miami na Amurka.

    Babu cikakken bayani game da yawan mutanen da ke cikin bangaren da ya rupta da safiyar yau.

    Wani da ya shaida alamarin ya yi karin bayani inda ya ce na leka ta taga ba bu abinda na gani.

    Na dauka hadari ne ko wani abu, kuma a lokacin da kura ta lafa abin ginin ya ruguje hotunan farko sun nuna wani yaro da aka ciro daga cikin baraguzan ginin kuma rahotani sun ce akalla mutum daya ya mutu.

  13. Jirgin soja ya yi hatsari a Nairobin Kenya

    Wani jirgin helikwafta na soja ya yi hatsari a kusa da Nairobi, babban birnin Kenya.

    Ma'aikatar Tsaro ta Kenya (KDF) ta ce ana gudanar da ayyukan ceto yanzu haka.

    Ana gudanar da ayyukan gwaji ne a lokacin da jirgin ya faɗo a yankin Ngong, a cewar sanarwa daga KDF.

    Akwai mutum kusan 20 a cikin jirgin, kamar yadda jaridar Standard ta ruwaito.

  14. Najeriya: An tura mata 'yan Civil Defence su kare makarantu daga harin 'yan bindiga

    Hukumar tsaro ta Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC) a Najeriya ta sanar da tura dakarunta mata domin kare makarantu daga hare-haren 'yan fashin daji masu satar ɗalibai a jihohin ƙasar.

    Kwamandan hukumar, Ahmed Audi, shi ne ya bayar da umarnin tattara su a ranar Laraba da ba su horo na wata ɗaya da kuma ba su kayan aiki a dukkan jihohin ƙasar guda 36 tare da Abuja.

    Ya ce tura dakarun wani ɓangare ne na shirin tsare makarantu na Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida da kuma Ministan Cikin Gida Rauf Aregbesola, wanda "ya umarci kwamandan da ya fito da tsari don kawo ƙarshen matsalar".

    "Biyo bayan yawaitar hare-hare da kuma garkuwa da ɗalibai a makarantu a ɓangarorin ƙasar nan, NSCDC ta yi wani nazari kan makarantu a faɗin ƙasar nan," a cewar wata sanarwa.

    Sanarwar ta ƙra da cewa "bayanan da muka samu za su taimaka wa dakaru wajen gudanar da aikinsu."

    Dubban ɗalibai ne da malamansu 'yan bindiga suka sace daga makarantu musamman a yankin arewacin Najeriya tun daga Disamban 2020.

  15. Tsohon Shugaban Philippines Benigno Aquino ya rasu

    Tsohon shugaban kasar Philippines, Benigno Aquino, ya rasu da sanyin safiyar Alhamis yana da shekara 61 a duniya.

    An kai shi asibiti da sassafe agogon kasar, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

    Tsohon shugaban na jam'iyyar Liberal da ake yi wa lakabi da suna 'Noynoy', ya fito ne daga zuri'ar masu karfin faɗa-a-ji ta fuskar siyasa, wanda ke adawa da salon mulkin Shugaba Ferdinand Marcos.

    A shekarar 1983 aka kashe mahaifinsa wanda dan majalisar dattawa ne a kasar.

    Wakilin BBC ya ce a lokacin da Beningno Aquino yake shugaban kasa ya kawo sauye-sauyen tattalin arziki, ya kuma yi kokarin magance matsalar cin hanci da rashawa.

    Mahaifiyarsa mai suna Corazon ta zama shugabar kasa karkashin jam'iyyar 'People Power' lokacin juyin-juya-halin da aka yi a shekarar 1986.

    Ana jimawa ba a ga mnarigayi Benigno Aquino a bainar jama'a ba tun bayan mika mulki ga shugaba Rodrigo Duterte a 2016.

  16. Amurka da EU sun yi Allah-wadai da harin Ethiopia da ya 'kashe' fararen hula

    Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) da Amurka sun yi Allah-wadai da harin da aka ce Ethiopia ce wato Habasha ta kai ta sama, wanda ya yi sanadiyyar kisan gwamman fararen hula a yankin Tigray.

    EU ta kira harin "mai matuƙar tsoratarwa" wanda aka hari fararen hula "da gangan".

    Sai dai rundunar sojan Ethiopia ta musanta kai wa farar hula hari amma ta tabbatar da cewa ta kai wa mayaƙan Tigray People’s Liberation Front (TPLF) sabbin hare-hare ta sama.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce a gudanar da bincike mai zamaan kansa da kuma bayar da damar kai magunguna ga waɗanda lamarin ya ritsa da su.

    An yi imanin cewa harin na Togoga ya kashe mutane da dama da kuma raunata wasu. Ƙungiyar agaji ta Red Cross ta ce ta taimaka wajen tseratar da mutanen da aka jikkata.

  17. Rundunar sojan Najeriya ta gargaɗi Sheikh Gumi kan zargin da ya yi mata

    Rundunar sojan Najeriya ta bayyana kalaman Sheikh Ahmad Gumi a matsayin "abin ɓacin rai da takaici" na cewa jami'an tsaro na haɗa kai da 'yan bindiga wajen aikata laifuka.

    Yayin da ya bayyana a kafar talabijin ta Arise TV ranar Laraba, malamin addinin Musuluncin ya zargi sojoji da sassauta wa 'yan fashin daji da ke addabar mazauna yankunan Najeriya.

    Ya ce 'yan bindigar ba za su iya samun makamai ba ba tare da taimakon jami'an tsaron ba.

    Sai dai da yake mayar da martani ga zarge-zargen, kakakin rundunar Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ya ce kalaman "na yunƙurin ɓata sunan dakarun sojan Najeriya ne da kuma sadaukarwar da suke yi".

    Ya yi kira ga manyan ƙasa da su mayar da hankali wajen nuna kishin ƙasa da kuma gina zaman lafiya "sama da zama 'yan barandan ɗaiɗaita ƙasar, abin da ka iya ta'azzara matsalar tsaron da ake fama da ita".

    A cewarsa: "Yayin da rundunar soja ba za ta kare ɓata-garin cikinta ba, dole ne mu bayyana ƙarara cewa ba za ta amince da duk wani yunƙuri na zagon ƙasa ba ko kuma taimaka wa abokan gaba daga duk wani jami'inta, yayin da tuni dokoki suka tanadi hukunci."

  18. Duk wanda muka kama da cin hanci sai mun hukunta shi - Babandede

    A Najeriya, shugaban hukumar kula da shige da fice ta ƙasar ya zargi wasu daga cikin ma'aikatan hukumarsa da karɓar cin hanci daga baƙin haure, inda suke barin su su zauna a ƙasar ba bisa ƙa'ida ba.

    An ga Muhammad Babandede a wani bidiyo a makon nan lokacin wata ziyarar aiki a jihohin da ke kan iyakar ƙasar yana nuna ɓacin ransa kan rashin gudanar da aikin ma'aikatansa yadda ya kamata.

    Ba kasafai ake jin manyan jami'an tsaro a Nijeriya suna ƙalubalantar na ƙasa da su a bainar jama'a kan cin hanci da rashawa ba.

    Abdussalam Ibrahim Ahmed ya tuntuɓi Muhammad Babandede ta wayar tarho game da ko me ya yi zafi a wannan karo?

    Saurari bayanin da ya yi wa BBC da Hausa idan kuka latsa hoton ƙasa:

  19. Gwamnatin Jihar Oyo ta umarci bokaye su lalubo maganin matsalar tsaro

    Gwamnatin JIhar Oyo da ke kudancin Najeriya ta bai wa bokayen da ke jihar umarnin su ɗauki kowane irin mataki domin kawo ƙarshen matsalar tsaro a jihar.

    Kwamishinan Yaɗa Labarai Dr Wasiu Olatunbosun ne ya bayar da umarnin ga majalisar masu maganin gargajiya ta jihar a madadin Gwamna Seyi Makinde.

    Ya tabbatar musu da cewa gwamnatin jihar za ta ba su dukkan goyon bayan da suke buƙata domin taimakawa wajen samo maganin matsalar.

    Matsalar garkuwa da mutane don neman kuɗin fansa ta karaɗe kowane yanki na Najeriya, ciki har da yankin kudu maso yamma inda ƙabilar Yarabawa ke da rinjaye mai yawa.

    Kazalika, yankin na fuskantar rikicin manoma da makiyaya ƙari a kan ƙungiyoyi masu fafutikar ɓallewa daga Najeriya da nufin kafa ƙasar Yarabawa ta Oduduwa.

  20. Masu iƙirarin jihadi sun kai hari a Mozambique

    Wata majiya daga sojojin Mozambique ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa masu ikirarin jihadi sun kai sabon hari a kusa da arewacin garin Palma.

    Jami'an tsaro sun ce saboda wannan ta sanya dole jirgin helikwafta ɗauke da sojojin da za a kai yankin ya yi saukar gaggawa sakamakon matsalar da ya samu, sai dai har yanzu babu cikakken bayani kan wadanda lamarin ya rutsa da su.

    A jiya Laraba ne kungiyar raya kasashen kudancin Afirka ta amince da tura dakaru kasar domin taimaka wa sojin Mozambique shawo kan matsalar masu tayar da kayar bayan da ke kara faɗaɗa ayyukansu a kasar musamman yankin Cabo Delgado mai arzikin iskar gas.

    Tuni masana sha'anin tsaro suka fara maraba da matakin.