Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Hukumar alhazan Najeriya za ta mayar wa maniyata kuɗaɗensu

Wannan shafin na kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Babu 'yan zanga-zanga a Ojota ta Jihar Legas

    A Jihar Leags, ana iya ganin 'yan sanda ƙalilan a Ojota, wurin da masu zanga-zanga suka ce za su taru a yau.

    Wani jami'in ɗan sanda a wurin ya faɗa wa wakilin BBC cewa tun a daren jiya Shugaba Buhari ya saka hannu kan wata doka da ta haramta gudanar da zanga-zangar. Sai dai BBC ba ta tabbatar da sahihancin iƙirarin nasa ba.

  2. Bikin Ranar Dimokuraɗiyya a Najeriya

    Yayin da ake bikin Ranar Dimokuraɗiyya a Najeriya yau Asabar, 12 ga watan Yuni, ana sa ran faruwar wasu abubuwa a yau ɗin.

    Daga cikinsu akwai jawabin Shugaba Muhammadu Buhari, wanda tuni ya gabatar da ƙarfe 7:00, da kuma zanga-zangar da wasu matasa suka yi alƙawarin gudanarwa.

    Ya zuwa yanzu dai babu rahoton wata zanga-zanga mai ƙarfi a Abuja da kuma Legas, yayin da jihohin ƙasar da dama suka sanar da hana yin ta.

  3. Ana zargin gwamnatin Trump da satar bayanan wayoyin 'yan adawa

    Ma'aikatar shari'a ta Amurka tana gudanar da bincike kan yunƙurin jami'an gwamnatin Donald Trump na samun bayanan wayar wasu manyan 'yan jam'iyyar Democrat daga kamfanin Apple.

    Ana tunanin hakan ya kasance wani ɓangare na binciken da ake yi kan katsalandan ɗin da Rasha ta yi a zaben shugaban Amurka na 2016.

    Wakilin BBC ya ce 'yan Democrat na kiran da a tilasta wa manyan jami'an gwamnatin Trump bayar da bahasi kan batun a gaban majalisar dokokin kasar.

    'Yan majalisa biyu, Adam Schiff da Eric Swalwell, sun ce an faɗa musu cewa an miƙa bayanan wayoyinsu har da na iyalansu.

  4. Ƙarin mutum 24 sun kamu da korona a Najeriya

    Sabbin alƙaluma daga hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya sun nuna cewa mutum 24 ne suka kamu da cutar korona ranar Juma'a a ƙasar.

    Hukumar NCDC ta ce sabbin kamuwar sun fito ne daga jiha biyar ciki har da Abuja, babban birnin ƙasar, sannan kuma babu wanda cutar ta yi ajalinsa.

    Jihohin su ne: Legas mai mutum 12, Gombe mai shida, sai kuma Abuja da Kaduna da Rivers masu biyu-biyu kowaccensu.

    Ya zuwa yanzu, NCDC ta ce jumillar mutum 167,051 ne suka harbu da cutar a Najeriya, 2,117 daga cikinsu sun rasu sannan an sallami 163,430 bayan sun warke daga cutar.

  5. Barka da hantsi

    Maraba da shigowa shafin rahotanni kai-tsaye. Kuna tare da Umar Mikail a wannan safiya ta Asabar, da fatan an fara hutun ƙarshen mako lafiya.