Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Twitter ya nemi sasanci da gwamnatin Najeriya – Lai Mohammed

Wannan shafin na kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Fauziyya Tukur and Awwal Ahmad Janyau

  1. Masu iƙirarin jihadi sun sace gwamman yara a Mozambique

    Ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi sun sace gwamman yara, mafi yawansu mata a shekarar da ta gabata in ji ƙungiyar Save the Children ta Burtaniya.

    Ƙungiyar ta ce a ƙalla yara 51 ne aka sace a lokacin rikici da ya raba dubban mutane da muhallansu.

    Haka kuma ta ce akwai yiwuwar adadin yaran ya fi haka.

    Ƙungiyar ta bayyana damuwarta kan irin waɗannan sace-sacen na yara inda ta ce abun na ƙara ta'azzara kuma yana da ban tsoro.

    Shugaban ƙungiyar ya ce sace-sacen na cikin manyan laifukan da suka shafi cin zarafin yara a lokacin rikici kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta ce.

    Ƙungiyar ta yi kira da a gaggauta sako yaran sannan a kama kuma a hukunta masu aikata laifin.

    Masu iƙirarin jihadi sun kwashe sama da shekara uku suna ayyukansu a arewacin Mozambique, suna sare kan mutane da kai hare-hare a ƙauyuka da birane da ƙona gidaje.

    Sama da mutum 700,000, sama da rabinsu yara ne, sun rabu da muhallansu a shekarun baya-bayan nan dalilin masu ta da ƙayar baya.

  2. Isra'ila za ta bari a gudanar da gangamin Yahudawa a birnin Ƙudus

    Gwamnatin Isra'ila ta ce za ta ba da izinin gudanar da gangamin da Yahudawa yan kishin kasa za su yi a birnin Kudus amma ta dage taron zuwa makon gobe.

    A ranar Litinin ne yan sanda suka ki amincewa da bukatar wadanda suka shirya gangamin ta tsara bi ta yankin Larabawan Isra'ila saboda dalilai na tsaro.

    Kungiyar Hamas ta yi gargadin cewa tattakin na iya haifar da wani sabon rikici bayan na watan da ya gabata.

    Ofishin Firaministan Isra'ila ya ce za a gudanar da gangamin bayan samar da tsarin da zai karbu a wajen masu shirya gangamin da kuma yan sanda.

  3. Bankin Duniya ya ce gwamnatoci su ƙara ba matasa damar samun ayyukan yi

    Bankin duniya ya yi kira kan gwamnatoci da su bunkasa damarmakin matasa na samun ayyukan yi tare da ba su horo domin su farfado daga bugun da annobar korona ta yi musu.

    Mataimakiyar shugaban bankin Mamta Murthi ta shaida wa BBC cewa lamarin zai iya shafar makomar mutum fiye da biliyan daya.

    Ta ce yan kasa da shekara 25 su wannan annoba ta fi shafa. Lamarin ya shafi karatunsu sannan wasu na iya samun aiki a masana'antun da annobar ta yi wa illa matuka.

  4. Sudan ta cire tallafin man da ake shigarwa ƙasar

    Sudan ta cire duk wani tallafi kan man da ake shigowa da shi kasar lamarin da ya sa farashin danyen mai da na dizel ya ninka .

    Ma'aikatar kudin kasar ta ce tallafin na janyo wa gwamnatin kashe dala biliyan daya duk shekara.

    Ta ce duk da karin baya-bayan nan, farashin danyen mai a Sudan na cikin mafi kankanta a fadin kasashen Afirka. Kara farashin man a baya dai ya janyo zanga-zanga a kasar.

    Garanbawul din da ake a fannin tattalin arziki tun bayan hambarar da gwamnatin Omar al-Bashir shekara biyu da ta gabata ya haifar da karyewar darajar kudin kasar da hauhawar farashin kayayyaki.

  5. Trump ya yabi Najeriya kan dakatar da Twitter

    Tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya yaba wa Najeriya kan dakatar da shafin sada zumunta na Twitter a ƙasar.

    A wata sanarwa da shugaban ya fitar ya ce "Ina yi wa Najeriya murna da haramta amfani da Twitter saboda shafin ya haramtawa Shugabanta amfani da shi."

    Sai dai Twitter bai haramta wa Shugaban Buhari amfani da shafin ba, illa dai ya cire wani sakon Tweet ne da shugaban ya wallafa kan masu iƙirarin ɓallewa daga ƙasar, sannan ya dakatar da shugaban tsawon awa 12.

    Haka kuma, Trump ya yi kira ga sauran ƙasashe da su bi sawun Najeriya wajen taƙaitawa ko haramta amfani da Twitter da Facebook. Dama dai Trump ba ya iya amfani da shafukan biyu saboda haramcin da suka sa masa.

    Ya ce shafukan suna hana ƴancin tofa albarkacin baki.

    A sanarwar tasa, ya ce "da na sani da na yi haka a lokacin da nake shugaban ƙasa, sai dai ya ce bai yi ba ne saboda shugaban kamfanin Facebook Mark Zuckerberg na yawan yabonsa a lokacin da ya ke mulki.

  6. Buɗewa

    Barkanku da kasancewa da mu a wannan shafin wanda zai kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta da ma sauran kasashen duniya.