Ƙarin mutum 42 sun kamu da cutar korona a Najeriya
Ƙarin mutum 42 sun kamu da cutar korona a Najeriya cikin awa 24 da suka wuce, a cewar hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a ƙasar.
Da wannan sabbin alƙaluman, jumillar waɗanda suka kamu da cutar tun watan Fabarairun 2020 sun zama 166,061.
Sai dai babu wanda ya rasa ransa a ranar ta Talata.
Sabbin mutanen da suka kamu da cutar sun fito ne daga jihohi takwas da suka haɗa da Legas (14) da Gombe (11) da Ebonyi (5) da Kano (5) da Abuja (4) da Edo (1) da Kaduna (1) da Rivers (1).
Ya zuwa yanzu, cutar ta yi ajalin mutum 2,067, sai kuma 156,492 da aka sallama bayan sun warke.