Ƙarin mutum 28 sun kamu da korona a Najeriya
Ƙarin mutum 28 sun kamu da cutar korona a Najeriya ranar Alhamis, a cewar hukumar yaƙi da yaɗuwar cutuka ta ƙasar, NCDC.
Bisa alƙaluman da ta wallafa, sabbin kamuwar sun fito ne daga jihohi shida na ƙasar har da Abuja.
Jihohin su ne: Legas (10), Rivers (7), Akwa Ibom (7), Delta (2), Abuja (2), Kaduna (1).
Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 165,301 ne suka kamu da cutar a Najeriya, 2,065 sun mutu da kuma 155,424 da aka sallama bayan sun warke.