Abin da shugabannin Afirka suka ce kan mutuwar Idriss Deby
Shugabannin Afrika Chadi sun bayyana kaɗuwarsu da alhini bayan samun labarin mutuwar shugaban ƙasar Chadi, Idriss Deby, wanda aka harba a filin daga lokacin da ya jagoranci sojojin kasar yaƙi da yan tawaye.
Shugaban rikon kwarya na MaliBah Ndaw, ya ce mutuwar Deby babban rashi ne a yaƙida kasashen sahel ke yi da mayaƙan jihadi.
Shugaban Nijar, Bazoum Mohamed, ya bayyana Deby a matsayin mai nuna sadaukarwa a yaƙi da ta'addanci, yayinda shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya yaba da irin rawar marigayi Deby ya taka a yaƙi da mayaƙan Boko Haram.
Shugaban Kamaru Paul Biya ya kira mutuwar Deby a matsayin babban rashi ga Chadi da tsakiyar Afrika da kuma Afrika baki ɗaya.
Biya ya yi Allah wadai da rikicin da har ya kai ga rasa ran Idris Deby.
Shugaban Jamhuriyar Congo Felix Tshisekedi wanda shi ne shugaban Tarayyar Afrika ya ce “Chadi da Afrika ta yi babban rashi.”
Mutuwar Deby ta zo ne bayan sanar da shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugabanci kasar karo na shida.
Sojoji sun ce ɗansa Mahamat Idriss Deby Kaka ne zai riƙe shugabanci zuwa lokacin wani sabon zaben a shekara mai zuwa.