Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Buhari ya yi Allah wadai da yunƙurin juyin mulki a Nijar

Wannan shafin na kawo maku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da sauran ƙasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Nasidi Adamu Yahaya and Awwal Ahmad Janyau

  1. An kawo ƙarshen matsalar ruwan famfo a Abuja

    Hukumomi a birnin Abuja, babban birnin Najeriya sun ce sun kawo ƙarshen matsalar ruwan famfo da ta addabi wasu sassa na birnin bayan tsawon kwana 12.

    Unguwannin da lamarin ya fi shafa sun haɗa da Ushafa da Kubwa da Dutsen Alhaji da Katampe da wasu sassa na Jabi da Gwarinpa da wasu sassan Garki.

    Lamarin ba ƙaramin sanya mutanen yankunan cikin tasku ya yi ba, musamman waɗanda ba su da rijiyoyin burtsatse.

    Wasu mazauna yankunan sun tabbatar wa da BBC cewa yanzu sun samu ruwan bayan kusan mako biyu.

    • Kuna iya karanta taskun da mazauna birnin suka shiga a nan
  2. Karen Joe Biden ya sake cizon ma'aikacin White House

    Karen da ke fadar shugaban Amurka mai suna Major ya sake cizon wani mutum 'yan kwanaki bayan ya dawo daga wurin horo a farkon watan nan.

    Mai magana da yawun Uwar Gidan Shugaban Ƙasa Jill Biden ya ce "bisa fargabar abin da ka iya faruwa" likitoci sun duba wani ma'aikaci kafin ya koma aiki.

    Major shi ne ƙarami daga cikin karnukan Shugaba Biden da ake yi wa laƙabi da German Shepherds kuma su ne karnukan aikin ceto na farko a Fadar White House.

    "Kare ne mai ban sha'awa," in ji Joe Biden.

    Mai magana da yawun Biden, Michael LaRosa, ya ce: "Har yanzu Major yana ci gaba da sabawa ne da muhallin da yake ciki kuma ya taɓa cizon wani a lokacin da yake wucewa."

    Kafar talabijin ta CNN ta ruwaito cewa karen ya ciji wani ma'aikacin hukumar kula da wuraren shaƙatawa, abin da ya sa sai da ya dakata da aiki likitoci suka duba shi.

  3. Labarai da dumi-dumi, An kama wasu sojoji a Nijar bayan yunƙurin 'juyin mulki'

    Wata majiyar tsaro ta shaida wa kamfanin labarai na AFP cewa an kama wasu sojoji a Jamhuriyar Nijar biyo bayan yunƙurin juyin mulkin da wasu dakaru suka yi a daren Laraba.

    Har yanzu babu cikakken bayani game da abin da ya faru yayin da birnin Yamai ya kasance cikin shirin ko-ta-kwana.

    Tun misalin ƙarfe 3:00 aka fara jin harbe-harben kuma an ɗauki tsawon kusan minti 15 ana yi.

    Jami'an tsaron fadar shugaban ƙasa ne suka daƙile yunƙurin, wanda ya faru ƙasa da kwana biyu kafin rantsar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Mohamed Bazoum.

  4. Sojoji ne suka yi yunƙurin juyin mulki a Nijar

    Yunƙurin juyin mulki ka iya zama dalilin da ya haifar da harbe-harbe a kusa da Fadar Shugaban Ƙasar Nijar a daren Laraba.

    Tun misalin ƙarfe 3:00 aka fara jin harbe-harben kuma an ɗauki tsawon kusan minti 15 ana yi.

    Jami'an tsaron fadar shugaban ƙasa ne suka daƙile yunƙurin, wanda ya faru ƙasa da kwana biyu kafin rantsar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Mohamed Bazoum.

    Sai dai gwamnati ba ta tabbatar da yunƙurin juyin mulkin ba ya zuwa yanzu.

    Tarihin Nijar wadda ke ɗaya daga cikin ƙasashe mafiya talauci a duniya, cike yake da juyin mulki na soja da kuma hare-haren 'yan bindiga masu iƙirarin jihadi da ke sanadiyyar rasa rayuka.

  5. Ba lallai ne Buhari ya miƙa mulki ga mataimakinsa ba - Fadar Shugaban Ƙasa

    Ba lallai ne sai Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya miƙa mulki ga mataimakinsa ba sakamakon tafiya Landan da ya yi, a cewar fadar shugaban ƙasa.

    Mai taimaka wa Buhari na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Garba Shehu, shi ne ya bayyana hakan a yammacin Talata yayin da ya bayyana ta cikin shirin Politics Today a kafar talabijin ta Channels.

    Ya ƙara da cewa mai gidan nasa bai karya wata doka ba don bai miƙa mulki ga Farfesa Yemi Osinbajo ba saboda ya fita daga ƙasar ne na 'yan kwanaki kawai.

    "Zai ci gaba da aiki duk daga inda yake," in ji Garba Shehu.

    "Abin da doka ta tanada shi ne, idan shugaban ƙasa zai kai kwana 21 ko fiye a waje, to sai ya miƙa mulki. A irin wannan yanayi na yanzu bai zama dole ba."

    Buhari ya yi balaguro zuwa Birtaniya a lokuta da yawa tun bayan hawansa mulki, amma wannan ne karon farko da ya je ƙasar tun bayan ɓullar annobar korona.

    Fadar shugaban ta ce ana sa ran zai koma Najeriya a makon farko na watan Afrilu mai kamawa.

    A 2017, ya shafe kwana 103 yana jinya a Landan, inda Osinbajo ya zama muƙaddashin shugaban ƙasa.

  6. An yi wa ɗan uwan shugaban ƙasa ɗaurin rai-da-rai bisa safarar ƙwayoyi

    An yanke wa dan uwan shugaban kasar Honduras Juan Orlando Hernandez hukuncin daurin rai-da-rai a gidan yari saboda fataucin miyagun kwayoyi.

    Masu shigar da kara a New York sun ce Tony Hernandez, wanda ya taba zama dan majalisa a Hoonduras, ya kasance babban jigo a daya daga cikin manyan kungiyoyin masu safarar hodar ibilis a duniya.

    An kama shi da laifin da ake tuhumarsa da aikatawa ne a watan Oktoban 2019, inda ake zarginsa da fataucin fiye da tan 180 na hodar ibilis zuwa Amurka.

    Wakilin BBC ya ce Shugaba Hernandez ya musanta hannu a safarar miyagun kwayoyin, yana cewa shari'ar wata makarkashiyar siyasa ce kawai.

  7. Ƙarin mutum 121 sun kamu da korona a Najeriya ranar Talata

    Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 121 da suka kamu da cutar korona a ƙasar ranar Talata.

    Bisa sabbin alkaluman hukumar, Legas ce ke kan gaba a yawan wadanda suka kamu da cutar a kasar da mutum 40.

    Alƙaluman hukumar sun nuna cewa an samu mutum 15 a birnin Abuja, da gwajin da aka yi musu ya nuna cewa sun kamu, abin da ke nufin cewa jihar ce ta biyu a wannan rana.

    A jihar Katsina an samu mutum 12 yayin da aka samu 11 a jihar Kaduna dake arewa masu yammacin kasar da aka tabbatar da cewa sun kamu da korona.

    Ga yawan waɗanda suka kamu a wasu jihohi:

    • Imo-8
    • Kebbi-8
    • Nasarawa-8
    • Delta-7
    • Edo-3
    • Osun-3
    • Rivers-3
    • Ekiti-1
    • Jigawa-1
    • Kano-1

    Zuwa yanzu dai adain wadanda suka kamu da cutar a Najeriya jimlatan ya kai 162,762 , ko da yake daga cikinsu an sallami 151,532 , sai kuma wasu 2,056 da su kuma suka mutu.

  8. Asalamu Alaikum

    Masu bibiyarmu barkanku da hantsin Laraba - ta bawa ranar samu.

    Ku biyo mu ku samu labaran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman a Nijar da Najeriya har ma da maƙotansu.

    Umar Mikail ne ke ƙaddamar da shafin a wannan lokaci.