An kashe matashiya 'yar shekara 20 a zanga-zangar Myanmar
An kashe mutum na farko a zanga-zangar Allah-wadai da juyin mulkin da sojoji suka yi a ƙasar Myanmar, inda aka harbi wata matashiya a ka.
Tun a makon da ya gabata ne aka jikkata Mya Thwe Thwe Khaing mai shekara 20 a lokacin da 'yan sanda suka yi yunƙurin tarwatsa masu zanga-zangar da ruwa da harsashin roba da kuma mai kisa.
Sai dai harbin da aka yi mata a kanta ne ya yi ajalinta, a cewar ƙungiyoyin kare haƙƙi.
An kwana biyu ana zanga-zanga a Myanmar biyo bayan juyin mulkin da ya tumɓuke Aung San Suu Kyi daga mulki.
Asibitin da ke birnin Nya Pyi Taw ya tabbatar da mutuwarta da misalin ƙarfe 11:00 na dare agogon ƙasar.