Za a gudanar da zaɓe a Falasɗinu a karon farko cikin shekaru 15
Ɓangarorin Falasɗinawa sun amince da tsare-tsare don gudanar da zaɓukan ƴan majalisar dokoki da na shugaban ƙasa a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da Zirin Gaza, a cewar kafofin yada labarai na Falaɗinu.
Bayan tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu da ke adawa da juna - Fatah da Hamas - wakilansu sun yi wata ganawa a Alƙahira wadda aka fara ranar 8 ga watan Fabrairu.
An sa za a gudanar da zaɓen majalisa a watan Mayu sannan za a yi na shugaban ƙasa a Yuli.
A cewar wani kwamiti kan zaɓukan, Falasɗinawa miliyan 2.36 a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da Zirin Gaza ne ke iya kaɗa kuri'a.
An gudanar da zaɓen majalisar dokoki na karshe a Falasɗinu ne a 2006 kuma Hamas ne suka yi nasara. Kuma su ne ke mulkin Gaza tun 2007 lokacin da suka yi nasara a wata karawa da makamai da Fatah.