Matar da
aka harba a kai lokacin gudanar da zanga-zangar nuna adawa da juyin mulkin da
soji suka yi a Myanmar na cikin mawuyacin hali a asibiti da ke Nay Pyi Taw
babban birnin kasar.
Mya Thwe
Thwe Khaing, mai shekaru 19, ta samu rauni a ranar Talata lokacin da ‘yan sanda
suka yi kokarin tarwatsa masu zanga-zanga ta hanyar amfani da harsasan roba da
na gaske da kuma motar ruwan zafi.
Ta samu
raunin ne daga harbin da aka yi mata da harsashin gaske, kamar yadda kungiyoyin
kare hakkin dan adam suka bayyana.
Akwai wasu
rahotanni samun munanan raunuka bayan da ‘yan sandan suka kara kaimi wajen yin
amfani da karfin tuwo kan masu gangamin amma har yanzu ba a samu asarar rayuka ba.
Dubban
mutane ne suka fita kan titina domin gudanar da zanga-zangar nuna kin jinin juyin
mulkin, da ya kawo karshen mulkin gwamnatin dimokaradiyya ta Aung San Suu Kyi,
duk kuwa da kafa dokar haramta taruwar jama’a da kuma ta hana fita da dare da
aka yi.
Zanga-zangar
ta fara gudana ne da safiyar Laraba, har na tsawon kwanaki biyar a jere, inda
kungiyoyin ma’aikata da dama suka hallara a birnin na Nay Pyi Taw domin
gangamin.