Gwamnatin Najeriya ta rage farashin man fetur
Gwamnatin Najeriya ta rage farashin man fetur da naira biyar biyo bayan matsin lamba daga haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙwadago.
Ministan Ƙwadago, Chris Ngige, shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan wata ganawa da ƙungiyoyin NLC da TUC a daren jiya Litinin a Fadar Shugaban Ƙasa.
Ya ce an rage farashin ne daga N168 zuwa N162.44 kan kowace lita ɗaya, wanda zai fara aiki daga ranar 14 ga watan Disamba.
Ana sayar da man kan N168 yanzu haka biyo bayan matakin da 'yan kasuwa suka ɗauka na ƙara farashin daga N147.67 zuwa N155.17 a watan Nuwamba. Ƙara ya biyo bayan matakin kamfanin da ke kula da kasuwancinsa na ƙara wa 'yan kasuwar farashi.
Chris Ngige ya ce an kafa wani kwamitin bincike da zai daidaita farashin man, yana mai cewa zai gabatar da rahotonsa ranar 25 ga watan Janairu.
"Tattaunawarmu ta yi armashi kuma NNPC, wanda shi ne babban kamfanin mai, da 'yan kasuwa sun amince cewa za a rage farashin man da N5 kuma ragin zai fara aiki ne daga Litinin mai zuwa," in ji Ngige.