''Mun ninka harajin da muke samu a jihar Kaduna''
Gwamnan jihar Kaduna Nasir Elrufa'i, ya ce jihar ta tara harajin da yawansa ya kai Naira kusan Naira biliyan 45 a shekarar 2019.
Hakan na nufin cewa jihar ta samu harajin da ya haura ninki biyu na abin da ta samu a shekarar 2016, wato shekaru huɗu da suka gabata, wato Naira Biliyan 23.
Gwamnan ya wallafa hakan ne a shafinsa na Twitter, inda ya ce hakan zai bawa gwamnatinsa damar aiwatar da ayyukan raya ƙasa da jama'a za su mora.
''Muna samun ƙaruwar haraji sannu a hankali cikin shekaru hudu da suka gabata, sannan samar da tsarin asusun ajiyar bai ɗaya na VAT ya taimaka ƙwarai wajen samun wannan nasara'' in ji gwamnan.