Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

An harbi wani malamin coci a Faransa

Wannan shafin na kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Lahadi idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin a yau:

    • Amurka ta yabi Najeriya kan taimakawa wurin ceto ɗan ƙasarta a Nijar
    • Ana ci gaba da zaƙulo waɗanda suka tsira a girgizar ƙasar Turkiyya
    • Sean Connery: Jarumin shirin James Bond ya mutu
    • An harbi wani malamin coci a Faransa
    • 'Yan tawaye sun kashe mutum 21 a Jamhuriyyar Dimokraɗiyyar Congo
    • Fashewa ta kashe yara biyu a Iraƙi

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai.

  2. Labarai da dumi-dumi, Covid-19: An saka sabuwar dokar kulle a Birtaniya

    Firaiministan Birtaniya ya sa sanar da saka sabuwar dokar kulle a ƙasar na tsawon wata guda sakamakon ƙara bazuwar cutar korona.

    Dokar za ta fara aiki ne daga ranar Alhamis. Mutane za su iya barin gidajensu ne kaɗai domin zuwa wuraren aiki ko motsa jiki ko kuma sayen kayan abinci.

    Saka dokar kullen na zuwa ne bayan adadin waɗanda suka kamu da cutar tun daga ɓullarta zuwa yanzu a Birtaniyar ya haura miliyan guda

  3. Belarus za ta rufe iyakokin ƙasarta na wani ɗan lokaci

    Belarus ta ce za ta kulle iyakokin ƙasarta na wani ɗan lokaci ga 'yan ƙasashen ketare daga ranar Lahadi.

    Kwamitin da ke kula da iyakar kasar, ya ce an ɗauki matakin ne saboda annobar korona.

    Sai dai matakin ba zai shafi mutanen da za su sauka a filin jirgin sama na babban birnin kasar ba, da kuma jami'an diflomasiyya da masu shigar da kayayyaki.

    Tun a watan Agusta ake fama da zanga-zanga a Belarus, bayan nasarar da shugaba Alexander Lukashenko ya samu a zaɓen ƙasar, wanda aka yi zargin yana cike da maguɗi.

  4. Za a sanar da sabuwar dokar kulle a Birtaniya

    Firaiministan Birtaniya, Boris Johnson na daf da yin jawabi ga 'yan ƙasar inda ake sa ran zai sanar da cewa za a sake saka dokar kulle karo na biyu a Ingila na tsawon wata ɗaya.

    Alƙaluman da aka samu na waɗanda suka kamu da cutar a ƙasar na nuni da cewa adadin ya ɗara mutum miliyan guda tun bayan da cutar ta fara ɓulla a ƙasar.

    Wasu jami'an gwamnati sun shaida wa BBC cewa za a buƙaci duka shaguna su kulle, sai dai shagunan kaɗai da suke sayar da muhimman kayayyaki za su ci gaba da zama a buɗe.

    Haka kuma za a buƙaci mutane su daina kai ziyara wurin 'yan uwansu da abokai.

    Sai dai ba kamar irin dokar da aka saka a baya ba, za a bar makarantu da jami'o'i su ci gaba da aiki.

  5. 'Yan tawaye sun kashe mutum 21 a Jamhuriyyar Dimokraɗiyyar Congo

    Jami'ai a Jamhuriyyar Dimokraɗiyyar Congo, sun bayyana cewa 'yan tawaye sun kashe aƙalla mutum 21 a gabashin ƙasar.

    Ana zargin ƙungiyar Allied Democratic Forces wato ADF ce ta kai hari ga abokan hamayyarta kafin ta kai hari a ƙauyen Lisasa da ke yankin Beni a arewacin lardin Kivu.

    'Yan tawayen sun ƙona wurare da kuma lalata wani asibiti.

    Ko a wannan makon sai da aka dora alhakin wani hari da aka kai kan ƙungiyar ta ADF wanda ya yi sanadin mutuwar mutum 15.

    Ƙungiyar ta kashe ɗaruruwan mutane a hare-haren ramuwar gayya tun bayan da rundunar sojin Congo ta kaddamar da yaƙi da su a bara.

  6. Tasirin zanga-zangar EndSars a Najeriya

  7. Labarai da dumi-dumi, An harbi wani malamin coci a Faransa

    Rahotanni daga Faransa na cewa an harbi wani malamin cocin kibɗawa a birnin Lyon na ƙasar.

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa maharbin ya tsere bayan aika-aikar da ya yi a ranar Asabar.

    An harbi malamin cocin sau biyu da misalin ƙarfe 4:00 na yammacin ƙasar a daidai lokacin da yake shirin rufe coci.

    Tuni dai jami'an agaji suka fara yi masa magani a cocin da aka yi harbin sakamakon raunukan da ya samu masu barazana ga rayuwarsa.

    Ko a ranar Alhamis sai da aka kashe mutum uku a wani hari da aka kai da wuƙa a birnin Nice na ƙasar.

    Hakazalika kwanaki kaɗan baya sai da wani mahari ya datse kan wani malamin makaranta a ƙasar bayan malamin ya nuna wa ɗalibansa wasu hotunan zanen ɓatanci da aka yi ga manzon Allah, Annabi Muhammad SAW.

  8. Sean Connery: Jarumin shirin James Bond ya mutu

    Jarumin min nan da ya fito a fina-finan James Bond, Sean Connery, ya mutu yana da shekara 90 da haihuwa.

    Jarumin, wanda ɗan asalin Scotland ne a Birtaniya, ya yi fice a fim ɗin James Bond kuma ya shafe sama da shekara 50 a masana'antar fim ana gwagwarmaya da shi.

    Rahotanni sun bayyana cewa Mista Connery ya mutu ne a cikin baccinsa a Bahamas bayan ya shafe lokaci mai tsawo ba shi da lafiya.

    Karanta cikakken labarin a nan:

  9. Ana ci gaba da zaƙulo waɗanda suka tsira a girgizar ƙasar Turkiyya

    Masu aikin ceto a Turkiyya na ci gaba da zaƙulo waɗanda suka tsallake rijiya da baya, bayan rushewar gine-ginen da ta biyo bayan gagarumar girgizar ƙasar da aka yi a ƙasar a jiya Juma'a.

    Akwai wata uwa da 'ya'yanta uku da aka zaƙulo bayan wani katon kankare ya taushe su.

    Magajin garin da lamarin ya faru ya jinjina wa masu aikin ceton, inda ya ce sun nuna bajinta wurin aikinsu duk da ruɗanin da ake ciki.

    Adadin mutanen da suka mutu sakamakon girgizar ƙasar ya kai 28.

    Tuni dai aka saka rumfuna na wucin gadi a fili da za su kasance a matsayin ɗakuna da wurin dafa abinci ga mutum dubu biyu na garin Izmir waɗanda suka rasa muhallinsu sakamakon lamarin.

  10. Amurka ta yabi Najeriya kan taimakawa wurin ceto ɗan ƙasarta a Nijar

    Hedikwatar tsaro ta Amurka ta tabbatar da sakin wani ɗan ƙasarta da aka yi garkuwa da shi a Jamhuriyyar Nijar, bayan wasu dakarun Amurkar sun kai samame wurin da ake riƙe da ɗan ƙasarta.

    Dakarun sun ceto Philip Walton a ƙasar da ke makwaftaka da Najeriya.

    A wani saƙo da ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya yi godiya ga gwamnatin Najeriya kan gudunmuwar da ta bayar da haɗin kai wurin ceto ɗan Amurkar a Nijar

    An yi garkuwa da shi ne a ranar Litinin a ƙauyen Massalata, kusan kilomita 10 daga iyakar Najeriya.

    Babu wani cikakken bayani kan waɗanda suka yi garkuwa da Mista Walton, amma masu iƙirarin jihadi da 'yan bindiga na cin karen su ba babbaka a yankin na Sahel, inda a wani lokaci suke garkuwa da mutane.

    Ko a kwanakin baya ma sai da aka kashe wasu 'yan Faransa da ɗan jagoransu biyu a jihar Tilaberi a yayin da suka je yawon buɗe ido.

  11. Lazio ta killace dukkanin 'yan wasanta saboda cutar korona

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafar Lazio mai buga gasar Serie A ta Italiya ta sanar da cewa ta killace dukkanin 'yan wasanta bayan gwajin cutar korona.

    Da ma tuni ƙungiyar ta rasa wasu 'yan wasan sakamakon cutar, inda ta saka ƙanana a wasan Champions League tsakaninsa da Brugge kuma suka tashi 1-1 ranar Laraba.

    Daga cikin manyan 'yan wasan da suka fara kamuwa da cutar akwai Ciro Immobile, wanda ya fi kowa zira ƙwallo a Serie A ta bara, da 'yan wasan tsakiya Luis Alberto da Manuel Lazzari, da Lucas Leiva da Djavan Anderson.

    Ƙungiyar ta ce ta sake yin gwaje-gwaje ranar Juma'a kuma "wasu daga cikin 'yan tawagar sun kamu da cutar". Sai dai ba ta bayyana sunan kowa ba.

    Wannan ne karon farko da Lazio ke bayyana 'yan wasanta da suka kamu da cutar bayan ta yi ƙorafi kan sakamakon gwajin cutar a makon da ya gabata.

    "An killace waɗanda suka kamu a gida yayin da tawagar za a killace sauran tawagar bisa kulawar likitoci," in ji sanarwar.

    Lazio ce ta 12 a teburin Serie A kuma za ta je Petersburg domin buga wasan Champions League da Zenit ranar Laraba mai zuwa.

  12. Fashewa ta kashe yara biyu a Iraƙi

    Wata fashewa ta yi sanadiyyar kashe yara biyu a kudancin Iraƙi a yau Asabar.

    Fashewar wadda aka hari wani bututun mai a yankin Muthanna, ita ce ta biyu bayan wadda aka kai a arewaci da ta sa aka rufe wani bututun.

    An fara gudanar da bincike kan lamarin na baya-bayan nan, wanda ya yi sanadiyyar jikkata mutum 28, a cewar wata kafar yaɗa labaran ƙasar.

    Harin ya zo ne bayan wanda aka kai a arewacin ƙasar, in ji wata sanarwa da gwamnatin yankin Kurdistan ta fitar ranar Juma'a.

    Sanarwar ta ce an dakatar da ayyukan safarar man fetur bayan wasu "'yan ta'adda" sun kai hari a yankin mai cin gashin kansa da ke kusa da tashar jiragen ruwa ta Ceyhan da ke Turkiyya ranar Laraba.

    Sai dai sanarwar ba ta bayyana a takamaimiyar ƙasar da fashewar ta faru ba ko kuma waɗanda suka kai harin.

  13. Kwamitin Legas na binciken cin zalin 'yan sanda ya zauna a rana ta uku

    Kwamitin da gwamnatin Jihar Legas ta kafa na jin bahasin abin da ya faru a harbe-harben da ake zargin sojoji sun yi yayin zanga-zangar EndSars a Legas ya ci gaba da zamansa a rana ta uku.

    A jiya Juma'a ne kwamitin ya ziyarci Lekki Toll Gate a cigaba da binciken zargin harbin masu zanga-zangar, inda mambobin kwamitin suka ɗebo kwanson harsasai da aka harba kuma suka ce za a bincike su.

    Tuni rundunar sojojin ta musanta zargin, tana mai cewa dakarunta ba su je wurin ba kwata-kwata sannan kuma ta ce Gwamnan Legas Babajide Sanwo-Olu ne ya nemi su fito tituna a ranar 20 ga watan Oktoba.

    A zamansa na yau Asabar, kwamitin ƙarƙashin jagorancin tsohuwar Mai Shari'a Doris Okuwobi zai saurari ƙorafi huɗu.

    Irin wannan kwamiti da wasu jihohi suka kafa ma sun fara nasu zaman, inda na Jihar Ogun ya ce ya karɓi ƙorafi 20 cikin mako biyu.

    An kafa kwamitocin ne domin bincike tare da biyan diyya ga waɗanda 'ya sanda suka ci wa zarafi ko kisa ba tare da haƙƙinsa ba a matsayin wani ɓangare na biyan buƙatun masu zanga-zangar neman gyara a ayyukan 'yan sandan Najeriya.

  14. MDD ta girmama 'yar Najeriya a matsayin 'yar sanda ta shekara

    An zaɓi wata 'yar Najeriya a matsayin waɗanda aka grimama da samun kyautar lambar yabo ta 'yar sanda ta shekara ta Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD).

    Catherine Ugorji wadda ta yi aiki da tawagar MDD a ƙasar Mali, an zaɓe ta ne sakamakon jajircewarta wurin rage yawan aikata laifuka a ƙasar.

    Jami'an MDD sun yabi ayyukan da ta aiwatar a rundunonin kiyaye zaman lafiya da kuma na filin daga.

    "Taya murna ga Cif Sufuritanda Catherine Ugorji ta 'yan sandan Najeriya da ke aiki da @UN_MINUSMA, wadda MDD ta zaɓa a matsayin ɗaya daga cikin mutum biyu da suka zo na biyu a kyautar 'yan sanda na shekara," a cewar ofishin MDD na Najeriya a shafinsa na Twitter.

    "Ɗabi'un Catherine Ugorji sun jaddada ƙa'idojin aikin MDD."

  15. Bikin cikar Gidan Arewa shekara 50 a Kaduna

    A cigaba da bikin cika shekara 50 da kafa Gidan Arewa, Gwamna Nasir El-Rufai ya gudanar da jawabinsa, yana mai cewa "shawarar da kwamitinsu [na jam'iyyar APC] ya bayar na sauya fasalin Najeriya ita ce mafita".

    Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, shi ne babban baƙo mai gabatar da lacca mai taken "Unfinished Greatness: Towards a More Perfect Union" wato "Cigaba da Nuna Nagarta: Zuwa ga Cikakken Haɗin Kai".

    Gwamnonin jihohin Ekiti da Jigawa da Sokoto da Kebbi da Kaduna na halartar taron tare da Sarkin Musulmi Sa'ad Abubkar.

    Sarkin Musulmin ya gabatar da Alhaji Ali Sarkin Mota, wanda shi ne direban Firimiya Sir Ahamdu Bello Sardauna a lokacin da yake Firimiyan Arewa, ga sauran manyan baƙi kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

  16. Belgium ta sake saka dokar kullen korona

    Belgium ta sanar da sake saka dokar kulle yayin da alƙaluma suka nuna cewa ta fi kowace ƙasa ƙaruwar masu kamuwa da cutar korona a Nahiyar Turai.

    Ayyukan da ba su zama dole ba da kasuwanci kamar na gyaran gashi, an umarce su da rufe daga ranar Litinin har zuwa tsakiyar watan Disamba.

    Haramun ne mutum sama da huɗu su taru a wuri guda a bainar jama'a.

    An umarci manyan kantunan sayar da kayayyaki da su sayar da kayan da ke da mahimmanci kaɗai sannan kuma mutum ɗaya aka bai wa damar zuwa daga kowane gida.

    Hutun makaranta na bazara, wanda aka saba yi daga Satumba zuwa Nuwamba, shi ma an ƙara shi har zuwa 15 ga Nuwamba.

    Kazalika, dokar hana fita da dare na nan daram, wadda tilasta rufe wuraren shan shayi da cin abinci.

    Gado 2,000 da aka tanada na jinyar masu buƙatar kulawar gaggawa sun cika da majinyatan cutar korona a ƙasar.

    Fiye da mutum 11,300 ne suka mutu a Belgium daga cikin mutum miliyan 11.5 na al'ummar ƙasar.

  17. Ba mu kashe kowa ba a Filato yayin satar kayan abinci – Sojojin Najeriya

    Hedikwatar tsaro ta sojojin Najeriya ta musanta zargin cewa sojoji sun kashe mutum huɗu a Jihar Filato yayin da matasa ke ƙoƙarin wawashe gidan tsohon Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Yakubu Dogara.

    A jiya Juma'a ne jaridar Vanguard ta ruwaito cewa dakarun rundunar Operation Safe Heaven (OPSH) sun halaka mutum huɗu tare da jefa gawarwakinsu a cikin kogi a garin Gwafan da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.

    "Wannan rahoto abin cutarwa ne ga sojojin Najeriya da kuma Operation Safe Heaven, waɗanda suka tabbatar da zaman lafiya a Filato," in ji hedikwatar tsaron cikin wata sanarwa a yau Asabar.

    Sai dai sanarwar ta tabbatar cewa sojojin sun je wurin da abin ya faru kuma har ma sun kama ɓarayin guda 30.

    "Saboda dalilai na tarihi, a ranar Lahadi 25 ga watan Oktoban 2020, 'yan daba sun shiga gidan tsohon kakaki a Lamingo domin yin sata," a cewar hedikwatar tsaron.

    Ta ci gaba da cewa: "Daga baya, dakarun OPSH da ke aikin dawo da zaman lafiya a Jihar Filato da kewaye suka isa wurin domin shawo kan lamarin. Cikin ƙwarewa da bin dokokin aiki, mun kama jumillar barayi 30 a wurin.

    "Bugu da ƙari, 'yan daba 114 aka kama, mata 21 da maza 93, da laifin sata. Idan ba a manta ba sai da aka gabatar da su ga manema labarai."

    An sha zargin rundunar sojojin Najeriya da kisan masu zanga-zangar EndSars da aka kwashe mako biyu ana yi a Lekki Toll Gate da ke Jihar Legas. Sai dai sun musanta zargin, suna masu cewa ba su je wurin ba gaba ɗaya.

  18. 'Yan adawa a Tanzania na son ƙasashen duniya su yi watsi da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa

    Babbar Jam'iyyar hamayya a Tanzania ta buƙaci gwamnatocin ƙasashen ƙetare da kar su amince da sakamakon zaɓen da aka fitar da ke tabbatar da nasarar Shugaba John Magafuli da gagarumin rinjaye.

    Hukumar zaɓe ta ce ya lashe zaɓen da kashi 85 cikin 100 na kuri'un da aka kada.

    Jam'iyyar Chadema ta bayyana sakamakon a matsayin "mugun aringizo".

    Shugaba Magafuli ya nemi wa'adi na biyu na shekara biyar, inda ya alkawarta sake bunkasa tattalin azriki ta hanyar ƙarasa manyan ayyukan da ya soma a wa'adinsa na farko.

  19. Girgizar ƙasa ta kashe mutum 20 a Turkiyya

    Masu aikin ceto a birnin Izmir na Turkiyya sun kwana suna hako bululluka masu ƙwari a cikin duhu domin lalubo wadanda ke da sauran numfashi bayan girgiza kasa ta afkawa Aegean a jiya Juma'a.

    Magajin garin Izmir Tunc Soyer yace gine-gine 20 suka rushe, masu aikin agaji sun bada rahoton mutuwar mutane 20, dari 7 kuma sun samu rauni.

    Girgizar kasar mai karfi maki 7 ta kuma lalata tsiribin Samos na Girka da ke kusa, da sanadi rayukan yara 2 bayan katanga ta rufta musu.

    Guguwar ta kuma haddasa tumbatsar teku inda ruwa ya malala a tittuna unguwannin da ke kuda da tashar jirgi.

  20. Cutar korona ta sake kashe mutum uku a Najeriya

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce adadin mutanen da annobar korona ta harba a ƙasar sun kai 62,691 bayan da aka gano ƙarin mutum 170 da suka kamu da ita ranar Jumma'a.

    NCDC ta ce kazalika, ƙarin mutum uku sun rasa rayukansu sakamakon cutar, wadda ta ɓulla a watan Fabarairun 2020 a ƙasar.

    Jihar Legas ce ker da adadi mafi yawa na mutanen da suka kamu a ranar Jumma'a da mutum 106, sai Abuja mai mutum 25.

    Oyo na da mutum 14, Edo da Kaduna na da mutum 7-7 kowaccensu da suka kamu da koronar.

    Ogun ta samu mutum 4 da suka kamu, sai Bauchi da Benue masu mutum 2-2.

    Jihohin Kano da Osun da kuma Rivers na da mutum ɗai-ɗai da suka kamu a kowacce jiha.

    Jumillar mutum 58,430 ne suka warke daga cutar kuma aka salleme su, yayin da 1,144 suka rasu zuwa yanzu.