Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Duk wanda bai dawo da kayan da ya sata ba za a rushe gidansa – Gwamnan Adamawa Fintiri

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a yau Talata 27 ga watan Oktoban 2020.

Rahoto kai-tsaye

Buhari Muhammad Fagge and Umar Mikail

  1. Shugaban ƙasar Kamaru ya yi Allah wadai da kisan kananan yaran da aka yi

    Shugaban ƙasar Kamaru Paul Biya ya yi Allah wadai da kisan wasu yara ƙanana da aka yi a wata makaranta a yankin rainon Ingila.

    Shugaban yakira wannan harin a matsayin “rashin imani da kuma laifi kan yaran da basu ji ba ba su gani ba”.

    Ya kuma ce ya umarci jami’an tsaro da su tabbatar da an kama wadannan mahara don girbe abin da suka shuka.

    Shugaban ya kuma aike sakon ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan a shafinsa na Twitter:

    Haka shi ma shugaban Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya shawarci hukumomi da su tabbatar sun nemo wadanda suka aikata wannan mummunan abu.

    “Ya kuma yi kira ga duk wasu kungiyoyi masu rike da makamai da su guji kai hari kan fararen hula domin mutunta dokar kasa da kasa kan ‘yancin dan adam.

  2. An kashe mutum bakwai a wani hari da aka kai wata makaranta a Pakistan

    Akalla mutum bakwai aka kashe sama da 50 suka jikkata a wani harin bam da aka kai wata makarantar addini a yankin Peshawar a Pakistan, in ji 'yan sanda.

    Hukumomin asibi sun ce waɗanda aka ashe maza ne matasa, da ke tsakanin shekara 20 da 30. gwamman mutane kuma sun jikkata ciki har da 'yan shekara 13.

    Babu wani dalili na kai harin kan ajin da ake koyar da karatun kur'ani.

    Har yanzu babu wata kungiya da ta ɗauki alhakin kai harin wanda ake ci gaba da bincike a kai.

    Yankin arewacin lardin Peshawar na kusa da iyakar Afghanistan, kuma na fuskantar matsalar tsaro daga Taliban a 'yan shekaun nan.

  3. Dakarun Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo sun kashe yan tawaye 27

    Dakarun Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo sun kashe ‘yan tawayen Rwanda da Burundi a wani rikici a yankin gabashin kasar, kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar Rwanda ya bayyana.

    Rundunar sojin ta yi ikirarin ta kori kungiyar ‘yan tawayen dake da karfi a yankin gabashin a yankin kudancin lardin Kivu.

    Rahotanni sun ce dakarun ƙasar sun hari kungiyoyin ‘yan tawayen na Burundi da na Red Tabara da ke ayyukansu a yankin gabashin ƙasar.

  4. An fara kaɗa ƙuri’ar zaben a Zanzibar tun da sanyin safiya

    An fara kaɗa ƙuri’ar zaɓe a Zanzibar na Tanzaniya, yankin da ke da kwarya-kwaryar cin gashin kai mai cike da tarihin rikicin zaɓe.

    Za a kaɗa kuri’a a babban birnin yankin a ranar Laraba.

    Zaben na yau da aka fara na jami’ai ne waɗanda za su sanya ido kan zaɓen, ciki har da turawan zaɓe da ‘yan sanda.

    Wannan ne karon farko da tsibirin na Zanzibar ke gudanar da zaɓe bayan gyaran da aka yi wa dokokin zaɓen.

    Sai dai ‘yan adawa sun soki gyaran da aka yi suna cewa hakan zai ba da damar yin maguɗin zaɓe ne kawai.Amma hukumar zaɓen kasar ta musanta wannan zargi

    Zaben yankin da aka yi a 2015 an soke shi ne saboda shugaban hukumar zaɓe ya ce cike yake da maguɗi.

    ‘Yan takarar 17 ne ke neman shugabancin yankin.

    An ma manyan su ne Maalim Seif Sharif Hamad na jam’iyyar adawa, da kuma Hussein Mwinyi, na jami’iyya mai mulki wanda ɗan tsohon shugaban ƙasar ne.

  5. Zanga-zanga ta ɓarke a Italiya kan dokar korona

    A na zazzafara zanga zanga a biranen Italiya don nuna adawa da kakaba sabbin dokokin kullen Korona.

    An samu rahotannin taho mu gama a biranen Milan da Turin da Naples da sauran birane.

    An rika jifar yan sanda an kuma wawushe shagunan al'umma a Turin.

    Rahotanni na cewa boren ya fara ne bayan da gwamnati ta ba da umurnin rufe gidajen abinci da wuraren sayar da barasa da sauran gidajen shakatawa saboda daƙile bazuwar annobar Korona.

    Annobar Korona na ci agba da bazuwa a kasashen Turai a karo na biyu.

  6. Akalla mutum 21 ne suka mutu a rikicin zaɓen ƙasar Guinea

    Akalla mutum 21 ne suka rasa rayukansu a tarzomar da ta biyo bayan zaben kasar Guinea a farkon wannan watan.

    An ci gaba da samun rikici tsakanin magoya bayan manyan jam’iyyun kasar da jami’an tsaro a karshen mako, yayin da hukumar zaɓen ƙasar ta tabbatar da nasar shugaba Alpha Conde a karo na uku.

    Jam’iyyar adawa, wadda ta bayyana kanta a matsayin wadda ta lashe zaɓen, ta ce Mista Conde ya karya dokar kasar saboda gyaran kundin tsarin mulkin da ya yi a watan Maris wanda ya ba shi damar ƙara tsayawa takara.

    Tuni Majalisar Dinkin Duniya da Kungiyar Kasashen Afrika suka aike da wakilai kasar ta Guinea domin shiga tsakani

  7. Amurka na son ƙara sayar wa da Taiwan makamai

    Gwamnatin Shugaba Trump ta sanar da yan majalisa cewa ta na son sayar da makamai na dala biliyan biyu ga Taiwan.

    Ba a jima ba da a ka yi huldar kasuwancin makaman irin wannan a tsakanin kasashen biyu, wadda ta fusata China har ta dauki matakin saka takunkumi ga wasu kamfanoni da ke kera wa Amurka makamai.

    Gwamnati a Taipei ta ce matakin Amurka na sayar mata da makamai ya nuna cewa da gaske ta ke yi wurin kare ta Taiwan, yayin da Chana ke dada karfin soji a yankin.

  8. Budewa

    Masu bibiyar mu a wannan shafi Buhari Muhammad Fagge ne ke fatan an wayi gari lafiya.

    Ku kasance da mu a wannan rana ta Talata domin kawo muku labarai da rahotanni kamar yadda muka saba.

    Batutuwan da suka shafi rayuwarku kai tsaye, da na kasashen ketare da sauran nahiyoyin duniya baki daya.