Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Atiku ya mayar wa Buhari da martani

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da makwabtanta.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba and Awwal Ahmad Janyau

  1. Gwamnatin Najeriya ta ba da umarnin buɗe makarantu

    Gwamnatin Najeriya ta ba da umarnin buɗe duka makarantu a ƙasar.

    Ministan ilimi, Adamu Adamu ya yi sanarwar yayin wani jawabi da ya yi a wani taron manema labarai a Abuja ranar juma'a.

    Ya shawarci duka makarantu su girmama ƙa'idojin sake buɗe makarantu.

    Jaridar Premium Times ta rawaito ministan na cewa za a buɗe makarantun sakandare na gwamnatin tarayya ranar 12 ga watan Oktroba yayin da makarantun gwamnati a jihohi da makarantu masu zaman kansu za su fitar da nasu jadawalin buɗe makarantu.

    Jihohi da yawa irinsu Legas da Oyo da Kano da Enugu tuni suka sanar da ranarkun komawar ɗalibai.

    A cikin watan Maris ne gwamnatin Najeriya ta ba da umarnin rufe makarantu a faɗin ƙasar saboda annobar korona.

  2. Nigeria@60: An kama ɗan sanda da masu zanga-zangar ƙin jinin gwamnati

    An tsare wani jami'in ɗan sanda a birnin Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya bisa cin zarafi tare da raunata wani ɗan jarida dake ɗaukar rahoto kan masu gudanar da zanga-zangar juyin juya hali kan abin da suka kira rashin shugabanci na gari a ƙasar.

    Gudanar da zanga-zangar ya zo dai-dai lokacin da ake gudanar da bikin cikar Najeriya shekara 60 da samun ƴancin kai ranar Alhamis.

    An kuma kama mutane da dama yayin zanga-zangar da aka gudanar a Legas da Osun.

    Wata sanarwa da ƴan sanda suka fitar a Legas ɗin ta ce yayin zanga-zangar, wani jami'in ɗan sanda mai muƙamin Inspekta Adadu Innocent ya yi amfani da sanda wajen ji wa ɗan jaridar rauni - ba tare da wata rashin jituwa ko fito na fito a tsakaninsu ba.

    A cewar hukumomi, an tsare ɗan sandan sannan za a tuhume shi kan saɓa doka domin ya zama izina ga wasu.

    Tuni kuma aka sallami ɗan jaridar da ya ji rauni wanda yake yi wa ɗaya daga cikin jaridun ƙasar - The Punch - aiki.

    Kimanin masu zanga-zanga 30 aka kama yayin zanga-zangar ƙin jinin gwamnatin da aka yi wa taken 'RevolutionNow' wadda aka gudanar ranar da ake bikin cika shekara 60 da samun ƴancin kai a Najeriya.

    Ƴan sanda sun bayyana masu zanga-zangar a matsayin marasa kishin ƙasa inda suka ce za a tuhumi mutanen da aka kama da laifukan da suka shafi haɗa taro ba bisa ƙa'ida ba da keta zaman lafiyar jama'a da kuma saɓa ƙa'idojin cutar korona.

  3. 'Shugaban Kenya ya ƙi amincewa Amurka ta kai wa al-Shabab hari a ƙasarsa'

    Shugaban Kenya Uhuru Kenyatta ya ce ba zai amince da hare-haren jiragen Amurka mara matuki ba kan ƴan al-Shabab a ƙasar, a cewar wani rahoton France 24.

    Shugaban wanda ya kai wata ziyara zuwa Faransa ya ce har yanzu bai samu irin wannan buƙatar ba.

    A watan da ya gabata Jaridar New York Times ta rawaito wasu majiyoyi da bata ambato sunansu ba na cewa sojojin Amurka na neman amincewa ta kai hare-haren irage mara matuka kan al-Shabab a gabashin Kenya.

    Rahoton na zuwa ƴan kwanaki kafin kotun soji a Somalia ta yanke wa wani ɗan IS hukuncin zama a gidan yari har tsawon rayuwarsa bisa rawar da ya taka a wani mummunan hari kan sansanin sojin Amurka a Kenya.

    Shi ne hari na farko da mayaƙan al-Shabab kan dakarun Amurka a Kenya.

    Amurka na yawan kai hare-hare ta sama a Somalia kan mayaƙan al-Shabab.

  4. Kun san shugabannin duniya da suka kamu da cutar korona?

    Labarin da ke cewa Donald Trump ya kamu da cutar korona abu ne da ka iya zama wani abin damuwa ga masu zaɓe a Amurka - amma ba su ne al'umar da suka fara ganin shugabansu ya kamu da annobar ba.

    Daga cikin shugabannin duniyar da wannan cuta ta kama sun haɗa da:

    Boris Johnson- Firaministan Burtaniya ya shafe kwana uku a sashen ba da kulawa ta gaggawa a watan Afrilu bayan ya kamu da cutar.

    Juan Orlando Hernández- Shugaban Honduras ya bayyana ta talbijin a watan Yuni cewa shi da mai ɗakinsa da wasu mataimakansa biyu sun kamu da annobar.

    Jair Bolsonaro- Shugaban Brazil shi ma ya kamu da cutar a Yuli bayan da gwajin da aka yi masa sau uku a baya ya nuna cewa baya ɗauke da cutar. Ya sha bayyana cutar wata almara har ma ya kira ta da wata "ƴar mura’.

    Alejandro Giammattei- Shugaban Guatemala ya kamu da ccutar korona cikin watan da ya gabata na Satumba bayan an yi masa gwaji sau shida. Ya bayyana cewa ya fuskanci ciwon jiki da kuma tari.

  5. Ana takun saƙa tsakanin babban abokin hamayyar Shugaba Magafuli da ƴan sandan Tanzania

    Ɗan takarar shugaban ƙasa a Tanzania Tundu Lissu ya ce zai yi burus da sammacin ƴan sanda yau Juma'a kuma a maimakon haka zai halarci wani taro da aka tsara gudanar da wakilan ƙasashen waje.

    Ya ce jam'iyyarsa ta Chadema ta samu wata wasiƙar sammaci daga ƴan sanda inda suke neman ya bayyana gaban shugaban gudanar da bincike a Dar es Salaam, babban birnin ƙasar da safiyar nan.

    Za a yi masa tambayoyi ne kan wasu kalamai da ya yi lokacin yaƙin neman zaɓe, kamar yadda takardar ta bayyana.

    Amma Mr Lissu ya ce takardar bata fito ta bayyana laifin da ya yi ba da har za a yi sammacinsa.

    A ranar 28 ga watan nan ne al'umar Tanzania za su fita zaɓen ƴan majalisa da shugaban ƙasa. Shugaba mai ci John Magafuli na neman ƙara shugabantar ƙasar na tsawon shekara biyar.

    Mr Lissu dai shi ne babban abokin karawar Magafuli a zaɓen.

  6. Coronavirus: Shugabannin Duniya na jajanta wa Donald Trump

    Shugabannin ƙasashen duniya sun fara miƙa saƙon jaje ga Shugaban Amurka Donald Trump da mai ɗakinsa bayan da aka tabbatar sun kamu da annobar korona.

    Firaministan Burtaniya Boris Johnson ya wallafa a shafinsa na Tuwita cewa yana yi wa Trump da matarsa addu'ar samun sauƙi. A lokacin da Johnson yake asibiti bayan kamuwa da korona, Trump ta Tuwita ya bayyana cewa yana tare da Johsnon a halin da yake ciki.

    Shi ma Firaministan India Narendra Modi wanda ya karɓi baƙuncin Trump yayin wata ziyarar aiki a farkon shekarar nan ya ce yana yi wa shugaban Amurkar da mai ɗakinsa "fatan samun sauƙi cikin gaggawa."

    Charles Michel wani jami'i a Kungiyar tarayyar Turai shi ma addu'ar samun sauƙi ya yi wa ma'auratan inda ya ce "cutar korona yaƙi ne da za mu ci gaba da yi. Kullum. Ko ina muke a duniya."

    Mai magana da yawun gwamnatin Faransa, ya ce kamuwar da Trump ya yi da annobar korona na nuna cewa "cutar bata raga wa kowa ba har da waɗanda suke nuna shakku game da cutar. Ina masa addu'ar samun sauƙi."

    Babban abokin hamayyar Trump a zaɓen watan Nuwamba, Joe Biden kawo yanzu bai ce komai ba amma a ranar Talata ne suka fafata a muhawararsu ta farko da suka yi gabanin zaɓen.

    Shugaban Rasha Vladimir Putin ya ce "kyawawan halaye da kuma kyakkyawan fata" na shugaba Trump zai taimaka masa wajen shawo kan cutar.

    Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce "ina miƙa fatan alherina ga Donald da Melania,". "Ina fatan za su warke daga cutar."

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce "Kamar miliyoyin Isra'ilawa da Sara [mai ɗakin Netanyahu] da kuma ni muna tunanin Shugaba Donald Trump da matarsa Melania Trump muna kuma yi musu addu'ar samun sauƙi".

  7. Kasuwannin hannayen jarin Amurka na kan hanyar faɗuwa bayan Trump ya kamu da korona

    Labarin Shugaba Donald Trump ya kamu da annobar korona ana saura wata ɗaya kafin zaɓen Amurka ya girgiza kasuwannin hannayen jari a ƙasar da ake sa ran za su fuskanci koma-baya idan aka fara hada-hada yau Juma'a.

    Da alama kasuwannin hannayen jari na Dow Jones da S&P da kuma Nasdaq za su yi ƙasa da kimanin kashi 1.5 kowannensu.

    Kasuwar hannayen jari ta Dow Jones na iya faɗuwa da maki 500, ita kuma Nasdaq za ta yi ƙasa da kashi 2 cikin ɗari yayin da S&P kuma za ta fuskanci koma-bayan kashi 1.7 cikin ɗari

    Wani babban mai tsara dabarun kasuwanci ƙungiyar IG Jingyi Pan ya ce, "lokaci ne mai mahimmanci a zaɓen Amurka," "Idan shugaban kasa ba ya nan a wannan lokacin, hakan na iya rikitar da harkar zaɓen."

  8. Cutar korona ta harbi ɗalibai 300 a Namibia

    Sama da ɗalibai 300 ne a Namibia suka kamu da cutar korona tun bayan buɗe makarantu a ƙasar.

    Ma'aikatar lafiyar ƙasar ta ce mafi yawan ɗaliban da suka kamu ƴan makarantar kwana ne.

    Ministan lafiyar Kalumbi Shangula ya ce ya kamata a riƙa bin shawarwarin likitoci domin hana yaɗa cutar a rufaffun wurare kamar makarantu.

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun rawaito cewa an samu ɓarkewar cutar a ɗaya daga cikin makarantun da ke yankin Oshikoto da ke da yawan masu fama da cutar.

    Tun a watan Maris ne ƙasar ta Namibia ta rufe makarantu saboda annobar sannan ta sake buɗe su a watan Yuni.

    Malamai da ɗalibai za su riƙa sa takunkumi kowane lokaci domin hana bazuwar cutar.

    Mutane 11,373 ne aka tabbatar sun kamu da korona a Namibia sannan mutum 123 kuma sun mutu.

  9. Barka da Safiya

    Masu bibiyarmu a wannan shafi assalamu alaykum, barka da wannan lokaci. Nabeela Mukhtar Uba ke fatan mun wayi gari lafiya a wannan rana ta Juma’a 2 ga watan Oktoban 2020.

    A yau ma za mu ci gaba da kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya.

    Za ku iya zuwa shafukanmu na sada zumunta - Facebook da Instagram har ma da Twitter domin ku tafka mahawara kan labaran.