Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Buhari zai tafi Guinea Bissau

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita and Fauziyya Kabir Tukur

  1. 'Yan sanda sun yi wa gidan shugaban 'yan adawa a Kamaru ƙawanya

    'Yan sanda a Kamaru sun yi wa gidan shugaban 'yan adawa a ƙasar ƙawanya.

    Sun yi wa gidan na Mista Maurice Kamto ƙawanya ne sakamakon zanga-zangar da ya haɗa a ranar Talata ta ƙin jinin gwamnati.

    Ana ta yaɗa wani bidiyo da ke nuni da motocin 'yan sanda jibge a ƙofar gidan shugaban.

    Shugaban ƙungiyar ta CRM ya shaida wa kafar yaɗa labarai ta Muryar Amurka cewa babu wanda ya buge shi ko kuma kama shi, amma yana tsoron za a kama shi da ya fita daga cikin gidansa.

    Mista Kamto, ya kira zanga-zangar ne don a kawo ƙarshen rikicin da ke faruwa a yankin renon Ingila da kuma kawo sauyi kan tsarin zaɓen ƙasar.

  2. 'Sau 21 aka yi ambaliyar ruwa bana a ƙasar China'

    Ƙasar China ta bayyana cewa sau 21 ana ambaliyar ruwa a bana, wannan shi ne adadi mafi yawa na ambaliya da aka yi a ƙasar sama da shekara 20.

    Ma'aikatar albarkatun ruwa ta ƙasar ta bayyana cewa sama da koguna 800 suka cika suka tumbatsa, inda 80 daga cikinsu suka cika suka kai yawan da ba su taɓa kaiwa ba.

    Tun daga farkon watan Yuli, hukumomi a China sun yi gargaɗi kan ruwan sama mai ƙarfi da za a yi na kwanaki 41, wanda hakan zai sa ba za a iya kauce wa ambaliyar ruwa ba.

    Masana kimiyya sun bayyana cewa adadin ruwan saman da ake yi a China ya ƙaru matuƙa tun tsakiyar shekarun 1990 inda suka ɗora alhakin ƙaruwar ruwan saman kan sauyin yanayi.

  3. Obasanjo ya halarci addu'ar uku ta Marigayi Sarkin Zazzau

  4. El-Rufai ya halarci addu'ar uku ta Marigayi Sarkin Zazzau

    Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El Rufai ya jagoranci ma'aikatan gwamnatin jihar zuwa wurin addu'ar uku, ta rasuwar Sarkin Zazzau, Marigayi Dakta Shehu Idris.

    Sarkin ya rasu ne a ranar Lahadi, bayan gajeruwar rashin lafiya inda kuma aka yi jana'izarsa da yammacin ranar.

  5. An kashe ɗaya daga cikin masu zanga-zanga a Kamaru

    An kashe wani mai zanga-zanga da raunata mutane da dama a Kamaru, yayin wata zanga-zangar ƙin jinin gwamnati da aka gudanar a ƙasar a ranar Talata, kamar yadda lauyan 'yan adawa a ƙasar ya bayyana.

    Mista Robert Amsterdam, wanda shi ne lauyan, ya wallafa wani bidiyo a shafin Twitter inda aka nuna wani mai zanga-zanga kwance bai motsi.

    Ya ce: "Mun samu labarin cewa an kashe aƙalla mutum ɗaya daga cikin masu zanga-zanga, inda 'yan sanda suka harbe shi a birnin Douala tare da kama mutane da dama,"

    Dama gwamnatin ta yi gargaɗi bisa zanga-zangar da shugaban 'yan adawa a ƙasar Maurice Kamto ya kira.

    Masu zanga-zangar dai na kira ne da a kawo ƙarshen rikicin da ke faruwa a yankin renon Ingila.

  6. Barkanmu da safiya

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Jama'a barkanmu da safiyar Laraba, 23 ga watan Agustan 2020. A yau ma za mu ci gaba da kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye a wannan shafin.

    Za ku iya ziyartar shafinmu na Facebook ko Twitter ko na Instagram domin bayyana ra'ayoyinku kan labaran da muka wallafa ko kuma tafka muhawara a kai.