Gwamna Wike ya bayyana abin da faru ga jami'in tattara zaɓen Ƙaramar Hukumar Orhionmwon
Gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike ya gudanar da wani taron 'yan jarida domin yin bayani kan abin da ya haifar da tsaiko wajen fitar da sakamakon zaɓen ƙaramar hukumar Orhionmwon.
Gwamna Wike wanda a baya ya bayyana gamsuwa da tsarin zaɓen gwamnan na Edo, ya ce ya yi mamaki kan yadda aka bayyana jami'in tattara sakamakon zaɓen ƙaramar hukumar ya yi ɓatan dabo.
Gwamnan ya bayyana haka ne a shafin gwamnan Edo Godwin Obaseki na Facebook.