Jirgi mara matuƙi na Daular Larabawa ya kashe sojoji 26 a Libiya
BBC ta samu wasu sabbin bayanai da ke nuna cewa wani jirgi mara matuƙi mallakar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ya kashe wasu masu koyon aikin soja 26 a Libiya.
Sojojin da aka kashe ba su riƙe da makamai a lokacin da aka kai musu hari a Tripoli babban birnin ƙasar a Janairun wannan shekara.
.A lokacin da aka kai harin, rundunar Janar Khalifa Haftar ta zagaye birnin na Tripoli. Janar Haftar dai na da kyakkyawar alaƙa da Daular Laraba.
Har yanzu ƙasar da ke yankin Gulf ba ta mayar da martani ba kan binciken da BBC ta gudanar.
Tun a baya dai, Janar Haftar da Daular Larabawa sun musanta kai wannan hari. Haka zalika Daular Larabawan ta musanta duk wani zargi da ake yi mata na cewa tana da hannu kan abin da sojojin Libiya ke yi.
Ƙasar ta ce tana goyon bayan shirin da Majalisar Ɗinkin Duniya take yi na samar da zaman lafiya.